Babbar Kotu Ta Yi Hukunci, Alkalai Sun Fara Cin Karo da Juna kan Taron PDP na Kasa

Babbar Kotu Ta Yi Hukunci, Alkalai Sun Fara Cin Karo da Juna kan Taron PDP na Kasa

  • Babbar kotun jihar Oyo ta yanke hukuncin da ya ci karo da na kotun tarayya mai zama a Abuja game da babban taron PDP na kasa
  • Hakan na zuwa ne bayan rikicin cikin gida ya kara dabaibaye babbar jam'iyyar adawa ta kasa, wanda ya kai ga darewarta gida biyu
  • PDP ta shirya gudanar da babban taron kasa wanda za a zabi sababbin shugabannnin jam'iyya a watan Nuwamba, 2025 a Ibadan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibadan, jihar Oyo - Kwanaki kadan bayan babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta dakatar da babban taron PDP na kasa, jam'iyyar ta samu wani umarni da ya saba wa hukuncin.

Kara karanta wannan

Jira ya kare: Hukumar NSIEC ta fitar da sakamakon zaben kananan hukumomin Neja

Babbar kotun jihar Oyo ta sahalewa jam'iyyar PDP ta kasa ta gudanar da babban taron kamar yadda ta tsara a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Shugaban PDP na kasa, Umar Damagum.
Hoton shugaban PDP na kasa, Umar Damagum a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja Hoto: @OfficialPDPNig
Source: Twitter

Jaridar The Cable ta tattaro cewa kotun ta yanke wannan hukunci ne a jiya Litinin, 3 ga watan Nuwamba, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotu ta yarda jam'iyyar PDP ta shirya taro

Kotun ta umarci shugaban PDP na kasa, Umar Damagum da sauran masu ruwa da tsaki su ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron yadda suka tsara.

Mai shari’a A.L. Akintola na babbar kotun Oyo, wanda yake jagorantar zaman kotun, ne ya bayar da wannan umarni a ranar Litinin.

Alkalin ya yanke wannan hukunci ne bayan ya saurari bukatar gaggawa da wani jigon PDP, Folahan Malomo Adelabi ya shigar a gaban kotun.

A karar, an bayyana PDP, Umar Damagum, gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) matsayin wadanda ake kara.

Bukatun da aka nema a kotun Oyo

Adelabi, ya roki kotu ta ba da umarnin wucin gadi da zai hana wadanda ake kara yin wani abu da zai iya rushewa, jinkirta ko dakatar da Babban Taron PDP da aka shirya yi a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Kara karanta wannan

An bai wa Tinubu hanyoyin yiwa Trump martani bayan barazana ga Najeriya

Adelabi ya kuma nemi kotun ta tilasta wa PDP, Damagum, da Gwamna Fintiri su bi kuma su mutunta ka’idojin da jadawalin ayyukan jam’iyyar da aka tsara domin gudanar da babban taron.

Shugaban PDP na kasa, Umar Damagum.
Hoton shugaban PDP na kasa, Ambasada Umar Damagum a hedkwatar jam'iyyar da ke Wadata Plaza, Abuja Hoto: @OfficialPDPNig
Source: Facebook

PDP: Hukuncin da kotun ta yanke

Alkalin ya amince da bukatar mai kara, inda ya umarci PDP da Damagum su ci gaba da shirye-shiryan taron kamar yadda suka tsara kafin yanke hukuncin karshe, in ji Tribune Nigeria.

Wannan hukunci na kotun ya biyo bayan takaddamar cikin gida da ta dabaibaye jam’iyyar PDP kan ko za ta ci gaba da taron ko kuma a dakatar da shi.

Da wannan sabon hukunci, watakila PDP za ta iya ci gaba da shirye-shiryenta na gudanar da babban taron zaben shugabanni na kasa a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

'Yan PDP sun yi zanga-zanga a Abuja

A wani rahoton, kun ji cewa rikicin shugabanci tsakanin tsagin Ministan Abuja, Nyesom Wike da bangaren Umar Damagum ya kara tsananta a PDP.

Wasu mambobin PDP sun yi zanga-zanga a babbar sakatariyar jam'iyyar PDP ta kasa da ke Wadata Plaza a Abuja ranar Litinin, 3 ga watan Nuwamba, 2025.

Kara karanta wannan

Rikici ya tsananta: Zanga zanga ta barke a sakatariyar jam'iyyar PDP da ke Abuja

Masu zanga-zangar sun zargi Damagum da rashin gaskiya da karkatar da harkokin jam’iyya, suna masu rantsuwa cewa za su kwace ikon sakatariyar PDP.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262