Babbar Magana: Kotu Ta Kwace Kujerar Dan Majalisar Tarayya daga Jihar Zamfara
- Kotu ta yanke hukuncin karbe kujerar dan Majalisar Gummi da Bukkuyum daga jihar Zamfara, Hon. Abubakar Gummi saboda ya koma APC
- Mai Shari'a Obiora Egwuatu ya ce abin da dan Majalisar ya yi na ficewa daga jam'iyyar da ya ci zabe ya saba wa dokar Najeriya
- Ya gargadi 'yan siyasa da cewa bai kamata su dauki sauya sheka a matsayin al'ada ba domin amana mutane suka dora masu
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige Dan Majalisar Wakilan Tarayya, Hon. Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga PDP zuwa APC.

Kara karanta wannan
Jiga jigai da 'yan Kwankwasiyya sama da 600 sun watsar da jar hula, sun koma APC a Kano
Hon. Abubakar, mai wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum daga Zamfara, ya rasa kujerarsa ne bayan da mai shari’a Obiora Egwuatu ya yanke hukunci a karar da aka shigar gabansa.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa alkalin ya yanke hukuncin cewa cewa sauya shekar da dan Majalisar ya yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC ya sabawa kundin tsarin mulki.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kotu ta sauke dan Majalisar Wakilai
A cikin hukuncin da aka yanke ranar Alhamis, mai shari’a Egwuatu ya umurci Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, da kada ya ci gaba da karɓar Abubakar a matsayin mamba mai wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma kotun ta umurci Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC) da ta shirya sabon zabe domin cike gurbin da Abubakar Gummi ya bari cikin kwanaki 30 daga ranar yanke hukuncin.
Abin da ya faru a zaman shari'ar
Tun farko, PDP da shugabanta na jihar Zamfara, Jamilu Jibo Magayaki, ne suka shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/CS/1803/2024 domin kalubalantar sauya shekar dan Majalisar.
Masu shigar da kara, ta hannun lauyansu Ibrahim Bawa (SAN), sun yi zargin cewa Abubakar ya bar PDP ba tare da wani rabuwar kai ba, sabanin abin da Sashe na 68(1)(g) na kundin tsarin mulki ya tanada.
A nasa bangaren, Hon. Abubakar Gummi ya kare kansa ta hannun lauyansa, inda ya ce ya koma APC ne sakamakon rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi a matakin kasa da na mazabarsa.
Kotu ta yi gargadi kan sauya sheka
Sai dai kotun ta yi watsi da wannan hujja, inda mai shari’a Egwuatu ya yanke hukunci cewa babu wani dalilin doka da ya halatta masa sauya sheka, don haka ya amince da bukatun masu shigar da kara.
A rahoton Vanguard, alkalin ya ce:
“’Yan siyasa su daina ganin sauya sheka a matsayin al’ada. Idan mutum yana son barin jam’iyya, kar ya tafi da amanar da mutane suka ba shi. Ba shi da ikon canja kuri’un da aka ba shi a jam’iyya guda zuwa wata jam’iyya.”

Source: Facebook
Yan Majalisa 6 daga Enugu sun koma APC
A wani labarin, kun ji cewa yan majalisar wakilai guda biyar daga jihar Enugu sun sanar da ficewarsu daga jam'iyyar PDP zuwa APC a hukumance.
Kakakin majalisar wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, ya karanta wasikun sauya shekar abokan aikinsa a zaman majalisar na ranar Alhamis, 30 ga watan Oktoba, 2025.
Wadanda suka sauya shekarsun haɗa da, Martins Oke, Anayo Onwuegbu, Nnamdi Agbo, Nnolim Nnaji da Mark Obetta.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

