"Ba Zan Boye Komai ba," Wike Ya Fadi Abin da Zai Fadawa Jonathan kan Batun Takara a 2027

"Ba Zan Boye Komai ba," Wike Ya Fadi Abin da Zai Fadawa Jonathan kan Batun Takara a 2027

  • Ministan Abuja ya ce a shirye yake ya fadawa Goodluck Jonathan ra'ayinsa idan ya nemi shawara kan batun sake neman takara a 2027
  • Nyesom Wike dai na daya daga cikin wadanda ba su goyin bayan tsohon shugaban kasar ya sake dawowa ya nemi mulkin Najeriya
  • Tsohon gwamnan ya gargadi Jonathan da cewa masu son dawo da shi, su ne dai wadanda suka yaudare shi a lokacin zaben 2015

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Najeriya – Ministan Harkokin Abuja, Nyesom Wike, ya ce zai faɗa wa tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan ra’ayinsa kai tsaye idan ya nemi shawararsa kan takara a 2027.

Kara karanta wannan

Nnamdi Kanu: Wike ya fadi sharadin zama shaidan shugaban IPOB a kotu

Wike ya bayyana cewa ba zai ji tsoron komai ba, zai fada wa Jonathan duk abin da ke ransa matukar ya tuntube shi game da fitowa takarar shugaban kasa a zabe na gaba.

Jonathan da Wike.
Hoton tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da Ministan Abuja, Nyesom Wike Hoto: Getty Images, @GovWike
Source: Twitter

Tsohon gwamnan na jihar Ribas ya bayyana haka ne a yayin tattaunawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shin Jonathan ya tuntubi Wike?

Ministan ya karyata jita-jitar da ke cewa Jonathan ya tattauna da shi kan takarar da ake so ya fito don sake neman mulkin Najeriya a 2027.

A cewar Wike:

“Jonathan bai gaya min zai nemi takara ba, bai kira ni ko sau ɗaya ba ya ce ana matsa masa lamba ya tsaya takara. Amma idan ya kira ni ya tambaye ni, zan faɗa masa ra’ayina da abin da nake ji a raina.”

Da yiwuwar Jonathan ya fito takara a 2027

Rahotanni sun nuna cewa ko da yake Jonathan bai bayyana aniyarsa ba, akwai alamar cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na ƙoƙarin ganin ya dawo takara a 2027.

Kara karanta wannan

Abin da Wike ya ce bayan yaɗa cewa Tinubu ya hana shi magana kan gwamnatinsa

A watan da ya gabata, tsohon ministan yada labarai, Farfesa Jerry Gana, ya bayyana cewa Jonathan zai tsaya takara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, in ji rahoton Leadership.

Gargadin da Wike ya yi wa Jonathan

Sai dai Wike, wanda tsohon yaron siyasar Jonathan ne, ya gargade shi da cewa kada ya bari ’yan siyasa su yi amfani da shi kamar yadda aka yi a zaben 2015.

A wani taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, Wike ya ce:

“Na san Jonathan sosai, yana da mutunci a idon duniya, kuma ya kamata ya kiyaye hakan. Waɗannan mutanen da ke ƙoƙarin jawo shi su ne waɗanda suka ruɗe shi a 2015.
“Waɗanda ke kira da ya tsaya takara yanzu, su ne waɗanda suka ci amanarsa a baya. Idan har ya bari su sake amfani da shi, to za su jefa jam’iyya cikin rudani.”
Ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike.
Hoton Ministan Harkokin Abuja, Nyesom Wike Hoto: @GovWike
Source: Facebook

Tinubu ya hana Wike magana da yawunsa?

A wani rahoton, kun ji cewa Nyesom Wike ya musanta rade-radin da ake yadawa cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hana shi magana kan gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

An tashi tawaga domin matsawa Jonathan ya hakura da takarar 2027

Wike ya ce shi ba mai magana ne da yawun Shugaba Bola Tinubu ba, sai dai yana bayyana ayyukansa a babban birnin Abuja a matsayinsa na minista.

Tsohon gwamnan ya ce aikinsa shi ne sanar da duniya abin da ke faruwa a karkashin gwamnatin Tinubu da kuma irin ci gaban da ake samu a birnin tarayya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262