Ana Jita Jitar Komawa ADC, Pantami Ya Sanya Labule da Shugaban PDP, an Ji Tattaunawarsu

Ana Jita Jitar Komawa ADC, Pantami Ya Sanya Labule da Shugaban PDP, an Ji Tattaunawarsu

  • Tsohon ministan sadarwa a Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami na ci gaba da karbar bakuncin manyan 'yan siyasa a gidansa da ke Abuja
  • Farfesa Pantami ya gana da shugaban jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya, Ambasada Umar Iliya Damagum a ziyararsa ta ban girma
  • Majiyoyi sun ce Pantami da bakin nasa sun tattaunawa kan ci gaban ƙasa da al’amuran mulki, noma, tattalin arziƙi da sauransu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Yayin da aka fara yada jita-jitar cewa Farfesa Isa Ali Pantami ya koma jam'iyyar hadaka ta ADC, malamin ya gana da shugaban PDP.

Shugaban jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya, Umar Iliya Damagum ya ziyarci tsohon ministan sadarwa, Farfesa Pantami a birnin Abuja.

Pantami ya gana da shugaban PDP
Shugaban PDP, Umar Damagum da Farfesa Isa Ali Pantami. Hoto: Peoples Democratic Party, Prof. Isa Ali Pantami.
Source: Facebook

Hakan na cikin wani faifan bidiyo da Farfesa Pantami ya wallafa a shafin Facebook da safiyar yau Juma'a 10 ga watan Oktobar 2025.

Kara karanta wannan

Amupitan: Jam'iyyar ADC ta aika sako ga sabon shugaban INEC da Tinubu ya nada

Rade-radin komawar Isa Pantami ADC

Wannan ganawar ta zo a daidai lokacin da wasu suka yi ta yadawa a kafofin sadarwa ciki har da Ahmed Tijjani Ramalan cewa Malam Isa Pantami ya bar APC zuwa ADC.

Hakan ya biyo bayan halartar wani taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ADC da Pantami ya yi a Abuja tare da Atiku Abubakar da David Mark da sauran jiga-jiganta.

Sai dai Legit Hausa ta yi bincike kan sahihancin komawar Pantami ADC inda ta gano babu inda tsohon ministan ya sanar da haka a hukumance har zuwa lokacin tattara wannan rahoto.

Pantami ya gana da shugaban PDP a Abuja

A cikin rubutun da ya yi, Pantami ya bayyana farin cikinsa bisa karbar bakuncin shugaban PDP da kuma tawagarsa a gidansa da ke Abuja.

Pantami ya rubuta cewa:

"Jiya da dare, na karɓi bakuncin Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa, Mai girma Ambasada Umar Iliya Damagum, a gidana da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi rashin dattijo: Tsohon jakada ya rasu yana da shekaru 92

"Tare da shi akwai ma’ajin jam’iyyar ta kasa, Alhaji Ahmad Yayari, tsohon Ministan Al’adu da yawon buɗe ido na Najeriya, Alhaji Muhammad Abubakar Sadiq.
Har ila yau, akwai tsohon darakta kuma ƙwararren masani a harkar kuɗi, Alhaji Bappa Ahmad Abdullahi."
Farfesa Pantami na ci gaba da ganawar siyasa inda suka yi zama da shugaban PDP
Farfesa Isa Ali Pantami yayin taro a Abuja. Hoto: Prof. Isa Ali Pantami.
Source: Facebook

Abubuwan da Pantami ya tattauna da Damagum

Farfesa Pantami ya bayyana cewa shi da Damagum da tawagarsa sun tattauna batutuwa masu muhimmanci da suka shafi noma da mulki.

Pantami ya ce kuma sun tabo batun tattalin arziki da bangaren ilimi da kuma abubuwan da suka shafi Arewacin Najeriya da hadin kan kasa.

A cewarsa:

"Mun tattauna muhimman batutuwa da suka shafi mulki, noma, tattalin arziƙi, ilimi, yankin Arewa da kuma haɗin kan Najeriya baki ɗaya.
Ina matuƙar godiya da wannan ziyara da mai girma Ambasada da tawagarsa suka kawo, wanda ta ƙara tabbatar da zumunci da haɗin kai a tsakaninmu."

Shugaban APC ya gana da Pantami a Abuja

Mun ba ku labarin cewa shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kai ziyara gidan Farfesa Isa Ali Pantami a Abuja inda suka tattauna batutuwa da dama.

Kara karanta wannan

Fiye da kwanaki 100 bayan rasuwarsa, an fara shiryen shiryen birne tsohon gwamna

Pantami ya bayyana cewa sun shafe shekaru tare a jami’a lokacin da Nentawe ke yin digiri na biyu, inda suka tuna lokutan farin ciki.

A cewar Pantami, sun tattauna kan ilimi, tattalin arziki, mulki da kuma jana’izar mahaifiyarsa, yana mai godiya bisa wannan muhimmiyar ziyara.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.