Atiku Ya Shirya Hakura da Takara da Tinubu a 2027? An Ji Gaskiyar Zance

Atiku Ya Shirya Hakura da Takara da Tinubu a 2027? An Ji Gaskiyar Zance

  • An yada wasu rahotanni masu nuna cewa Atiku Abubakar ya shirya hakura da takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027
  • Tsohon mataimakin shugaban kasan ya fito ya fayyace gaskiya kan batun cewa ya shirya janyewa matashi takara a zaben da ake tunkara
  • Atiku ya bayyana cewa sauya ma'anar abubuwan da ya fadi a cikin hirar da aka yi da shi cikin 'yan kwanakin nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi magana kan batun hakura da takara a zaben 2027.

Atiku Abubakar ya karyata ikirarin cewa zai janyewa matashi kafin zaɓen shugaban kasa na 2027.

Atiku ya musanta batun fasa takara a 2027
Tsohon mataimakin shugaban kasan Najeriya, Atiku Abubakar. Hoto: Mustapha Sule Lamido
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar a shafinsa na X a ranar Alhamis, 2 ga watan Satumban 2025.

Kara karanta wannan

Nigeria @65: Muhimman abubuwa 5 da Tinubu ya fada a jawabin ranar samun 'yanci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun da farko dai, Atiku ya riga ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Atiku ya bar jam’iyyar PDP wadda ya tsaya takarar shugaban kasa karkashinta a zaɓen shekarar 2023.

A watan Agusta kuma, Atiku da wasu manyan ‘yan adawa irinsu Nasir El-Rufai, Rotimi Amaechi, Peter Obi da sauransu, sun amince da yin amfani da jam’iyyar ADC domin kalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Me Atiku ya ce kan fasa takara?

A cikin sanarwar, Paul Ibe ya bayyana irin waɗannan rahotanni a matsayin sauya hirar da ya yi da aka yi da Atiku kwanan nan.

Paul Ibe ya ce nazari mai zurfi kan bidiyo da fassarar hirar ya nuna cewa Atiku bai taɓa faɗa, nunawa, ko ma ya yi nuni da cewa yana da niyyar janyewa wani takara ba.

“Ya zama wajibi a fayyace gaskiya kan wasu rahotanni da suka taso daga hirar da Mai girma Atiku Abubakar ya yi da BBC Hausa, kamar yadda wasu kafafen yaɗa labarai suka kawo."

Kara karanta wannan

Babbar magana: Atiku ya ce zai iya hakura da buga takara da Tinubu a 2027

“Bayan cikakken nazari kan bidiyo da rubutacciyar hirar, a cikin Hausa da kuma fassarar Turanci, a bayyane yake cewa babu inda tsohon mataimakin shugaban kasa ya faɗi, ko nunawa, ko ma ya yi alamun cewa yana shirin janyewa wani ba."
"Abin da Atiku Abubakar ya faɗa a fili kuma babu wani ruɗani shi ne cewa matasa, da kuma duk wani mai sha’awar tsayawa takara, suna da ‘yancin yin hakan."
"Ya kara jaddada cewa idan wani ɗan takara matashi ya yi nasara bayan zaben fitar da gwani na adalci, zai goyi bayan wannan ɗan takarar ba tare da wani jinkiri ba."

- Paul Ibe

Atiku ya ce bai da shirin fasa yin takara a 2027
Atiku Abubakar na jawabi a wajen wani taro. Hoto: @atiku
Source: Facebook

Atiku ya caccaki Shugaba Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya caccaki Shugaba Bola Tinubu.

Atiku Abubakar ya zargi gwamnatin Tinubu da yin rikon sakainar kashi da batun kare rayuka da dukiyoyin 'yan Najeriya.

Tsohon mataimakin shugaban kasan ya bayyana cewa mutane da dama sun koma masu bara duk da dumbin albarkatun da Najeriya take da su.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng