Shirin APC Ya Fara Rushewa, Babban Jigo da Magoya Bayansa Sun Fice daga Jam'iyyar

Shirin APC Ya Fara Rushewa, Babban Jigo da Magoya Bayansa Sun Fice daga Jam'iyyar

  • Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Yobe ta samu koma baya yayin da daya daga cikin manyan jiga-jiganta ya fice daga cikinta
  • Hon. Mohammed Bello, tsohon dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa ya mika takardar ficewarsa daga APC ga shugabannin jam'iyyar
  • Rahotanni sun nuna cewa jam'iyyun adawa na ADC da PDP sun fara zawarcin dan siyasar tare da magoya bayansa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Yobe - Babban jigon APC, wanda dan siyasa ne sananne a jihar Yobe, Hon. Mohammed Bello, ya fice daga jam’iyya mai mulki.

Hon. Mohemmed Bello ya bayyana matakin da ya dauka na raba gari da APC a matsayin “fita daga kangin da yake ciki.”

Tutar APC.
Hoton tutar jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya Hoto: OfficiaAPCNig
Source: Getty Images

Jigo da magoya bayansa sun bar APC

Bello, wanda tsohon ɗan takarar Sanatan Yobe ta Arewa (Zone A) ne a ƙarƙashin inuwar APC, ya sanar da ficewarsa tare da dimbin magoya bayansa, cewar rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Komai na iya faruwa: Shugaban APC ya sanya labule da Farfesa Pantami a Abuja

Dan siyasar ya tabbatar da hakan a wata wasika da ya aika wa shugaban jam’iyyar APC na mazabar Gwange, a birnin Damaturu.

A takardar, wacce ta shiga hannun manema labarai, Hon. Mohammed ya ce matakin da ya dauka ya fara aiki ne nan take.

Meya sa Hon. Mohammed Bello ya bar APC?

A wani bangaren wasikar, fitaccen dan siyasar ya ce:

“Na rubuto muku wannan wasiƙa ne don sanar da ku a hukumance game da shawarar da na yanke ta ficewa daga jam’iyyar APC daga yau.
"Ban yanke wannan shawara haka kurum ba, sai da na yi dogon tunani kan dabi’ata, akiduna da kuma inda jam’iyyar ta dosa.
"Bayan dogon nazari, na yanke cewa abin da yafi dacewa da ni da al’ummata shi ne na fice daga jam’iyyar APC a wannan lokaci.”

Hon. Mohammed Bello ya bayyana godiyarsa bisa damar da ya samu ta yin takara a tsawon lokacin da ya shafe a matsayin dan jam'iyyar APC.

Kara karanta wannan

Magoya bayan Peter Obi sun tanka bayan ADC ta ba'yan hadaka umarni

Ya ce mu'amala da gogewar da ya samu za su kasance masu amfani gare shi har abada.

Hon. Mohammed Bello.
Hoton fitaccen dan siyasa a jihar Yobe, Hon. Mohammed Bello Hoto: Hon. Mohammed Bello
Source: Facebook

ADC da PDP sun fara zawarcin dan siyasar

Bugu da kari, ya hada da katinsa na APC ya aika wa shugabannin jam'iyyar domin tabbatar da matakin da ya dauka.

A halin da ake ciki, majiyoyi sun bayyana cewa shigabannin jam'iyyar hadaka watau ADC sun fara zawarcin Mohammed Bello da magoya bayansa.

Ita ma, babbar jam’iyyar adawa ta PDP, ta fara ƙoƙarin jawo shi ya shiga cikinta a yayin da ake ci gaba da shirin babban zaɓen 2027, in ji rahoton Daily Post.

Gwamna Mbah na shirin komawa APC

A wani labarin, kun ji cewa Gwamna Peter Mbah na Jihar Enugu ya gama shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki.

Majiyoyi masu karfi da ke kusa da gwamnan sun bayyana cewa Peter Mbah ya amince zai koma APC ne bayan tattaunawa da wasu manyan jiga-jigai.

Wadanda suka taimaka wajen jawo gwamnan har ya amince da shiga APC sun hada da tsofaffin gwamnoni, Chimaroke Nnamani da Sullivan Chime.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262