Bayan Katoɓararsa, NNPP Ta Kori Jibrin Kofa daga Jam'iyya, Ta Jero Wasu Dalilai

Bayan Katoɓararsa, NNPP Ta Kori Jibrin Kofa daga Jam'iyya, Ta Jero Wasu Dalilai

  • Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta sanar da korar Abdulmumin Jibrin daga jam'iyyar saboda zargin yin adawa da ita
  • Shugaban jam’iyyar, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce nasarar Jibrin ta dogara ne da tallafin Kwankwasiyya da NNPP
  • Dungurawa ya ce Jibrin ya ƙi biyan kudaden jam’iyya kuma za su gurfanar da shi a kotu don karɓar hakkinsu bisa doka

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta dauki mataki mai tsauri kan dan majalisar tarayya daga jihar Kano.

Jam'iyyar ta tabbatar da korar Hon. Abdulmumin Jibrin, dan majalisar wakilai daga Kiru/Bebeji, bisa zargin adawa da jam’iyya da kuma kin biyan kudade.

NNPP ta fatattaki Hon. Jibrin Kofa daga jam'iyyar
Hon. Jibrin Abdulmumin tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso. Hoto: @KwankwasoRM.
Source: Twitter

Shugaban NNPP a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce korar ta biyo bayan kalaman Jibrin a kafafen yada labarai kan jam’iyya da shugabancinta, cewar Daily Trust.

Kara karanta wannan

Bayan Sanusi II ya gama digirin PhD, Abba zai jawo jami'ar London zuwa Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Dalilin' da ya jawo korar Jibrin daga NNPP

Rahotanni sun nuna hakan na zuwa kwana guda bayan Jibrin ya ce ba abin mamaki ba ne idan ya fice daga jam’iyyar.

Ya kuma jaddada cewa yana da ikon yanke shawara da kansa kan abin da ya dace da shi a siyasa a kowane lokaci.

Hon. Jibrin Kofa ya kuma tabbatar da cewa babu abin da zai hana Bola Tinubu lashe zaben 2027 da ake tunkara a Najeriya.

Jam'iyyar NNPP ta tonawa Hon. Jibrin asiri

Dungurawa ya bayyana Jibrin a matsayin “dan siyasa mai rauni” da nasararsa ta dogara ne kacokan da Kwankwasiyya da kuma dandalin NNPP.

Sanarwar ta ce:

“Idan har yana da ƙarfi sosai da ya lashe zabe a karkashin APC, amma ya kasa, sai da NNPP ta tallafa masa."

Ya ce an kafa kwamiti domin duba hirar Jibrin da Channels TV, amma daga baya maganarsa ta nuna ya tsallake iyaka gaba ɗaya.

Kara karanta wannan

Kano: Ciyaman ta sake jawowa Abba Kabir magana, yan sanda sun gayyace ta

Ya ce:

“Maimakon tattaunawa, ya ci gaba da yin aiki akasin muradunmu, ya bayyana biyayyarsa ga wasu a waje, wannan ya sa muka kore shi."
A karshe, NNPP ta kori Hon. Jibrin bayan katobarar da ya yi
Dan majalisar dokoki daga jihar Kano, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa. Hoto: Abdulmumin Jibrin.
Source: Facebook

Karin wasu zarge-zarge kan Hon. Jibrin

Dungurawa ya kuma ce Jibrin ya saɓa biyan kudaden jam’iyya da doka ta wajabta, inda suka kuduri aniyar gurfanar da shi a kotu.

“Za mu gurfanar da shi don dawo da abin da muke bin shi. Kowane mamba na da wajibin biyan kudin jam’iyya."

- In ji Dungurawa

Jam'iyyar NNPP ta bugi kirji kan karfinta

Game da jita-jitar komawarsa APC, Dungurawa ya ce hakan ba zai raunana NNPP ba, domin siyasa tana samun nasara ne da haɗin gwiwa, Tribune ta tabbatar.

Ya kara da cewa Kwankwasiyya na nan daram tare da jagoranta, Rabiu Musa Kwankwaso, kuma duk wani sauyi ba zai iya karya ƙarfinsu ba.

Kwankwaso: Hon. Jibrin ya fallasa 'yan APC

Kun ji cewa dan majalisar tarayya daga jihar Kano, Hon. Abdulmumin Jibrin ya yi magana kan siyasar Najeriya da zaben 2027.

Kara karanta wannan

"Ba laifin Tinubu ba ne," Dan Majalisa daga Kano ya yi magana kan matsalar tsaron Arewa

Hon. Jibrin Kofa ya bayyana cewa wasu shugabannin APC a Kano ba sa son Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga jam’iyyar.

'Dan majalisar ya ce tattaunawa kan makomar siyasar Kwankwaso na ci gaba, amma ya fi mayar da hankali wajen samar da gwamnatin hadin guiwa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.