APC Ta Shiga Matsala, Magoya bayan Jam'iyyar 50,000 Sun Sauya Sheka zuwa ADC a Sokoto

APC Ta Shiga Matsala, Magoya bayan Jam'iyyar 50,000 Sun Sauya Sheka zuwa ADC a Sokoto

  • Dubunnan magoya bayan jam'iyya mai mulki ta APC a karamar hukumar Gada, a jihar Sokoto sun sauya sheka zuwa ADC
  • Wadanda suka sauya shekar sun ce sun bar APC saboda gazawar gwamnatinta wajen magance matsalar tsaro da tattali
  • An ce fiye da mutum 50,000 suka shiga ADC, yayin da Sanata Abubakar Gada ya ce jam'iyyar hadaka za ta ceto Najeriya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Sokoto - Daruruwan mambobin jam’iyyar APC a karamar hukumar Gada ta jihar Sokoto sun sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Wadanda suka sauya shekar, sun bayyana takaici kan yadda gwamnatin APC ta gaza wajen magance matsalar tsaro da tsadar rayuwa da ta addabi al'umma.

'Dubunnan magoya bayan jam'iyyar APC ne suka koma jam'iyyar ADC a Sokoto
Gungun magoya bayan jam'iyyar ADC da suka gudanar da gangami bayan karbar 'yan APC a Sokoto. Hoto: Animashaun Salman
Source: UGC

Sanata ya tarbi masu sauya sheka zuwa ADC

A ranar 24 ga Agusta, 2025, tsohon sanata kuma jigon jam’iyyar ADC, Sanata Abubakar Gada, ya karɓi wadanda suka sauya shekar a Gada, inji rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Ambaliyar ruwa ta shiga gidaje 4521 a jihar Yobe, an rasa rayuka

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wajen taron, Sanata Gada ya bayyana wannan mataki a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwa domin ceto Sokoto da Najeriya daga rashin kyakkyawan shugabanci.

“Mutanenmu sun ƙuduri aniyar kuɓutar da kansu da ƙasarsu daga mulkin shekaru na gwamnati mai ci, kowa na da yakinin ADC za ta kawo sauyi mai ma'ana.” inji Sanata Gada.

Ta'addanci ya durƙusar da tattalin Sokoto

Sanata Gada ya jaddada yadda matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a yankin gabashin Sokoto, inda hare-haren ‘yan bindiga suka lalata harkar noma, wanda shi ne ginshikin tattalin arzikin yankin.

Sanata Gada ya ce:

“Rashin tsaro ya haifar da yunwa, talauci da rashin aikin yi. Mutanenmu ba za su iya yin noma cikin kwanciyar hankali ba yanzu.”

Masu sauya shekar sun maimaita waɗannan korafe-korafe a wajen taron, yayin da suka zargi APC da gazawa wajen fuskantar matsalolin, abin da ya sa suka koma ADC.

Kara karanta wannan

'Yan Majalisa 3 su fice daga NNPP, APGA, su sauya jam'iyya a Najeriya

ADC na samun karɓuwa a jihar Sokoto

Rahoton jaridar The Sun ya nuna cewa fiye da mambobin APC 50,000 ne suka sauya sheka zuwa jam'iyyar ADC a Sokoto, lamarin da ya girgiza jam’iyya mai mulki.

Sanata Gada ya bayyana cewa an samar da hadakar 'yan adawa domin dawo da zaman lafiya da farfaɗo da harkar noma da bunkasa tattalin arziki.

“Kowane ɗan Najeriya na da haƙƙin tsaro da wadatuwar abinci. Jam'iyyar ADC ta zo don tabbatar da hakan,” inji Sanata Gada.
Sanata Abubakar Gada, ya ce lokaci da ya yi da ADC za ta ceto Najeriya daga mulkin gwamnatin APC
Taswirar jihar Sokoto da ke Arewa maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

ADC za ta iya nasara a zaɓen 2027?

Da aka tambaye shi kan yiwuwar ADC ta kayar da APC mai mulki 2027, Sanata Gada ya ce ya dora yakininsa a kan ikon Allah.

“Mulki na Allah ne, ba na karfin jam'iyya ko gwamnati ba,” inji Sanata Gada, yana mai kira ga ‘yan Najeriya da su mara wa ADC don kawo sauyi a 2027.

Masu sharhi na ganin wannan sauya shekar a matsayin alamar raunin tasirin APC a Sokoto, inda ta saba da karfi a siyasa.

Kara karanta wannan

'APC ƙungiyar asiri ce,' Ƙusa a PDP ya jero manyan matsalolin jam'iyya mai mulki

"APC kungiyar asiri ce' - Jigon PDP

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim ya zargi APC da rashin akida, inda ya ce tsarin ta ya fi kama da na mulkin kama-karya.

Ya bayyana cewa APC ta jawo durkushewar tattalin arzikin Najeriya daga $570bn zuwa $300bn tare da karuwar matsalar tsaro.

Dakta Gbenga Hashim ya dage cewa PDP ce sahihiyar jam’iyyar dimokuraɗiyya, ya na mai neman ‘yan Najeriya su kawo sauyi a zaɓen 2027.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com