PDP Ta Samu Koma Baya, Tsohon Sanatan Kebbi Ya Fice daga Jam'iyyar

PDP Ta Samu Koma Baya, Tsohon Sanatan Kebbi Ya Fice daga Jam'iyyar

  • Jam'iyyar PDP mai adawa a jihar Kebbi ta samu nakasu bayan daga cikin manyan 'ya'yanta ya yi murabus
  • Sanata Isa Galaudu wanda ya taba wakiltar Kebbi ta Arewa a majalisar dattawan Najeriya, ya sanar da ficewarsa daga PDP
  • Tsohon dan takarar gwamnan na PDP a zaben 2019, ya ce daya daga cikin dalilinsa na fice daga jam'iyyar shi ne yadda abubuwa suka tabarbare

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kebbi - Tsohon sanata mai wakiltar Kebbi ta Arewa a majalisar dattawa, Isa Galaudu, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar PDP.

Isa Galaudu wanda shi ne dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PDP a zaɓen shekarar 2019, ya bayyana wannan mataki nasa ne a cikin wata wasika da ya rubuta mai ɗauke da kwanan watan ranar 20 ga watan Agusta, 2025.

Kara karanta wannan

"An yaudari 'yan Najeriya": Kungiya ta kinkimo aiki kan takarar Jonathan a 2027

Isa Galaudu ya fice daga jam'iyyar PDP
Hoton Sanata Isa Galaudu tare da hatimin jam'iyyar PDP Hoto: @Saddam_Jalingo
Source: Twitter

Jaridar TheCable ta ce ya aika da wasikar ne ga shugaban jam'iyyar PDP na mazabar Augie ta Arewa a jihar Kebbi, Muhammadu Aliyu Danbuga.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Isa Galaudu ya fice daga PDP

A cewar tsohon shugaban ma’aikatan shugaban majalisar dattawan, murabus ɗinsa daga jam’iyyar PDP ya fara aiki nan take, ba tare da wani jinkiri ba, rahoton The Punch ya tabbatar.

Ya ƙara da cewa ya dauki wannan matsaya ne bisa la’akari da abubuwan da ke faruwa a PDP a halin yanzu, da kuma sakamakon abin da ya bayyana rushewar jam’iyyar baki ɗaya.

"Na rubuto wannan wasika don sanar da kai cewa daga yau na yi murabus daga kasancewata ɗan jam’iyyar PDP. Wannan murabus ɗin ya fara aiki nan take."
"A bayyane yake cewa yanzu PDP tana ƙarƙashin ikon wasu ‘yan siyasa da ke cikin jam’iyyar da ke mulki a kasa.”

- Isa Galaudu

Isa Galaudu ya yi wakilci a matsayin Sanata daga 2011 zuwa 2015 a majalisar dattawa, inda ya wakilci Kebbi ta Arewa.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar ADC ta yi martani bayan an zarge ta da yaudarar 'yan Najeriya

Haka kuma, ya taɓa yin aiki a matsayin ɗaya daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa na jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto.

Jam'iyyar PDP na fama da rikice-rikice

Sanarwar ficewar Isa Galaudu daga PDP ta zo a wani lokaci da ake ganin jam’iyyar tana fuskantar kalubale iri-iri daga cikin gida da kuma daga waje.

Tsohon sanatan PDP a Kebbi ya bar PDP
Taswirar jihar Kebbi, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Yawancin masu sharhi sun bayyana cewa ficewar tsofaffin manyan jiga-jigan jam’iyyar kamar Galaudu da wani babban koma baya ne ga makomar PDP, musamman a Arewacin Najeriya.

A daidai lokacin da siyasar kasar nan ke kara zafi wajen shirye-shiryen 2027, wannan murabus ɗin ya sake jefa tambayoyi kan yadda PDP za ta iya tsayawa da ƙafafunta da kuma ci gaba da kasancewa babbar jam’iyyar adawa.

Jam'iyyar ADC ta soki gwamnonin PDP

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar ADC ta ragargaji gwamnonin PDP kan yin taron siyasa a jihar Zamfara.

Jam'iyyar ADC ta bayyana cewa taron da gwamnonin suka gudanar ya nuna rashin tausayi, duba da halin da Zamfara ke ciki na rashin tsaro.

Ta bayyana cewa ko kadan bai kamata gwamnonin na PDP su gudanar da taron siyasa a jihar Zamfara ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng