2027: Atiku Ya ba da Kafa, Ya Faɗi Abin da Ya Sa Yake Takarar Shugaban Kasa

2027: Atiku Ya ba da Kafa, Ya Faɗi Abin da Ya Sa Yake Takarar Shugaban Kasa

  • Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi magana kan takarar shugaban kasa a zaben 2027
  • Atiku ya ce ba ya da bukatar zama shugaban kasa dole, abin da yake nema shi ne ganin Najeriya ta gyaru
  • 'Dan siyasar ya bayyana hakan a wurin taron masu sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC a Lagos da ke Kudancin Najeriya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya magantu kan takararsa.

Atiku ya ce yana neman Najeriya ta inganta ne ba wai sai ya zama shugaban kasa ba dole ba.

Atiku ya tabbatar da abin da ya dame shi a Najeriya
Atiku Abubakar yayin taron masu ruwa da tsakin PDP a Abuja. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Facebook

Abin da Atiku ya fi so a Najeriya

Atiku ya bayyana hakan ne a wajen bikin maraba da sababbin wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC a Lagos ranar Asabar, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

2027: An zaɓi Sule Lamiɗo domin takara da Jonathan? Tsohon gwamnan ya magantu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Atiku, wanda Farfesa Ola Olateju ya wakilta ya ce abin da yake nema shi ne gwamnati nagari, ba mulki na dole ba.

Ya ce:

“Ina da shirin gina Najeriya ta inganta. Ba game da zama shugaban kasa ba ne, amma gwamnati mai iya yi wa jama’a aiki."

Olateju ya kara da cewa ADC ba jam’iyya ba ce kawai, sai dai wata tafiya ta ’yan Najeriya masu neman canji da sabuwar hanya mai kyau.

Ya ce:

“Ba siyasa irin ta da ba, wannan farawa ne, Atiku yana jagorantar sabuwar tafiya domin kyakkyawan makomar Najeriya.”
Atiku ya magantu kan batun takararsa a 2027
Atiku ya ce bai zama dole sai ya zama shugaban kasa ba. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Facebook

Atiku ya jero matsalolin Najeriya a yanzu

Olateju ya jaddada cewa, manufarsu ba wai Atiku ko wani ya zama shugaban kasa dole ba, amma Najeriya ta samu ci gaba da kwanciyar hankali.

Atiku ya nuna cewa, matsalolin da Najeriya ke fama da su, musamman cire tallafin mai da tashin farashi, za su kau da shugabanci nagari.

Kara karanta wannan

2027: Malamin addini ya 'gano' shirin Amurka domin cire Tinubu da ƙarfin tsiya

Ya ce, Allah zai yi amfani da hadin kan mambobin wannan tafiya wajen kawo sauyi da kyakkyawar makoma ga al’ummar Najeriya baki daya.

Kan batun wanda zai samu tikitin ADC a 2027, Atiku ya ce jama’ar jam’iyyar ne kawai za su tantance ta hanyar sahihin zabe.

Manufar jam'iyyar ADC kan zaben 2027

Atiku ya ce ba dole ya zama shugaban kasa bane, ko Obi, amma duk wanda ya ci ya zama wakilin muradun jama’a, cewar The Guardian.

Sababbin wadanda suka sauya sheka sun hada da Dr. Abimbola Ogunkelu, tsofaffin shugabannin PDP na Legas, da wasu shugabannin matasa na jam’iyyar.

An tarbi wadannan sababbin mambobin ne ta manyan jagororin ADC ciki har da Rauf Aregbesola, Sanata Kolawole Ogunwale da George Ashiru, shugaban jam’iyyar na jihar.

Atiku ya fadi yadda aka daure mahaifinsa

Kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi magana kan wasu darussan da ya koya a rayuwarsa.

Atiku Abubakar ya bayyana cewa saboda ƙin bari a sanya shi a makaranta, an taɓa ɗaure mahaifinsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma yi bayani kan yadda ya taɓa tsallake rijiya da baya lokacin da aka yi yunƙurin hallaka shi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.