2027: Shehu Sani Ya Ba Goodluck Jonathan Shawara kan Shigar Takarar Shugaban Kasa
- Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya shiga cikin masu ba Goodluck Jonathan shawara kan batun takara a zaben 2027
- Shehu Sani ya shawarci Goodluck Jonathan da kada ya sake tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 da ake tunkara
- Tsohon sanatan ya bayyana cewa abubuwa sun sauya sosai a jam'iyyar PDP wadda tsohon shugaban kasan ya lashe zabe a karkashinta a 2011
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya ba tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, shawara kan yin takara a zaben shekarar 2027.
Shehu Sani ya shawarci Goodluck Jonathan da kada ya sake tsayawa takarar shugaban kasa a zaɓen 2027.

Asali: Twitter
Shehu Sani, ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin 'Sunday Politics' na tashar Channels Tv, a ranar Lahadi, 18 ga watan Agustan 2025.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Goodluck Jonathan yana da damar takara
Goodluck Jonathan dai ya kasance mataimakin tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’adua na tsawon shekaru uku, kafin rasuwarsa.
Daga bisani Jonathan ya gaje shi a ranar 6 ga Mayu, 2010, har zuwa 29 ga Mayu, 2011. Daga nan kuma ya tsaya takara a karkashin PDP inda ya lashe zaɓen shugaban kasa, ya ci gaba da mulki har zuwa ranar 29 ga Mayu, 2015.
Jonathan ya sake tsayawa takara a 2015, amma ya sha kaye a hannun Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC.
A tsarin mulki, Jonathan har yanzu na da damar yin wa’adi guda na shekaru hudu idan ya so, sai dai bai nuna sha’awar sake tsayawa takarar ba.
Yayin da ake gab da zaɓen 2027, tattaunawa kan yiwuwar dawowar Jonathan ta kara ɗaukar hankalin ‘yan siyasa, musamman kasancewar ana muhawara kan batun shugaban kasa daga Kudu ya yi wa’adi daya.

Kara karanta wannan
'Zan iya soke zaɓen': Jonathan ya faɗi abin da ya kayar da shi a 2015 a hannun Buhari
Wace shawara Shehu Sani ya ba Jonathan?
Tsohon sanatan ya ce jam’iyyar PDP, wadda Jonathan ya yi amfani da ita wajen lashe zaɓen 2011, yanzu ba ta da haɗin kai kamar yadda take da shi a baya.

Asali: Twitter
"Duk lokacin da aka kusa yin zaɓe, sai sunan Jonathan ya taso. Amma duk da cewa dama tana hannunsa ya tsaya takara idan yana so, shawara ta gare shi ita ce kada ya yi hakan."
"Dalilin kuwa mai sauƙi ne, jam'iyyar PDP da ya sani a baya ba ita ce PDP ta yanzu ba."
“PDP ta yankin Kudu maso Yamma tana mara wa shugaban kasa baya. Wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar kuma suna cikin hadaka. Don haka jam’iyyar da ya sani a baya ta canza, bai kamata ya ɓata lokacinsa ba."
- Shehu Sani
Jonathan ya magantu kan zaben 2015
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya tuna baya kan abubuwan da suka faru a lokacin zaben 2015.
Goodluck Jonathan ya bayyana cewa an samu bambanci sosai kan yadda aka kada kuri'a yankin Arewa da Kudu, wajen yin amfani da katin tantance masu kada kuri'a.
Ya bayyana cewa da ya so, da ya soke zaben saboda yadda katin tantancewar ya rika kin yin amfani a Kudu.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng