An Dauko Batun Wanda Za a Nada a Matsayin Sabon Shugaban INEC kafin Zaben 2027

An Dauko Batun Wanda Za a Nada a Matsayin Sabon Shugaban INEC kafin Zaben 2027

  • A karshen shekarar 2025, wa'adin shugaban hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu zai kare
  • Bisa tanadin kundin tsarin mulki, shugaban kasa ne ke da ikon nada shugaban INEC, sannan Majalisar Tarayya ta tantance shi
  • Kungiyar Yiaga Africa ta bai wa Shugaba Bola Tinubu shawarwarar wanda ya kamata ya nemo, ya ba shi wannan aiki mai muhimmanci

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Kungiyar Yiaga Africa, ta shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya naɗa ƙwararre a matsayin shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).

Ta kuma bukaci shugaban kasa ya lalubo mutane masu nagarta ya nada su a matsayin kwamishinonin INEC, wadanda ke jagorantar harkokin zabe a jihohi.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Hoton Shugaba Tinubu a ofishinsa yana aiki Hoto: @aonanuga1956
Asali: Facebook

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa wa’adin mulkin shugaban INEC na yanzu, Farfesa Mahmood Yakubu, zai ƙare a ƙarshen wannan shekara da muke ciki.

Kara karanta wannan

Rikici ya kacame da Shugaban karamar hukuma a Neja ya maka Gwamna Bago a kotu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An fara ba Tinubu shawara kan kujerar INEC

Yiaga Africa ta bukaci Shugaba Tinubu da ya nemo mutane masu ƙwarewa da nagarta, wadanda ba su dogara da kowa ba, ya ba su shugabancin hukumar INEC.

Kungiyar ta bayyana haka ne a wani taron tattaunawa da aka shirya kan kare ’yancin hukumar INEC wanda ya gudana a ranar Juma’a a Abuja,

Babban Daraktan Yiaga Africa, Samson Itodo, ya yi gargadin cewa naɗin shugabanni ba tare da zurfin tunani ba na iya raunana hukumar zaɓe kuma ya lalata dimokuraɗiyyar Najeriya.

'Wadanda ya kamata a nada su jagoranci INEC'

Itodo ya jaddada cewa dole a kula sosai wajen sauyin shugabanci da ke tafe a INEC domin kada a dakushe hukumar wajen gudanar da ingantattun zaɓe.

“Ba wai kawai cika sharuddan kundin tsarin mulki na kasancewa mutum mai gaskiya da rashin son kai kadai ake so ba.

Kara karanta wannan

Jerin sunaye: Shugaba Tinubu ya amince da kafa sababbin jami'o'i 9 a Kaduna da wasu jihohi 7

"Muna bukatar mutanen da suka nuna ƙwarewa wajen gudanar da zaɓe, basira, fasaha, kuzari, da ƙarfin hali wajen kauce wa matsin lamba na siyasa," in ji shi.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da Farfesa Mahmud Yakubu.
Shugaban kasa, Bola Tinubu a fadar shugaban kasa, da shugaban INEC mai barin gado yana jawabi Hoto: @OfficialABAT, @INECNigera
Asali: Facebook

Yiaga Africa ta fadi tsarin da ya kamata a bi

Ya shawarci shugaban ƙasa da ya tabbatar da gaskiya a tsarin naɗa shugabannin INEC ta hanyar bayyana sunayen waɗanda ake son naɗawa kafin a tura su majalisar dokoki ta ƙasa.

Itodo ya bayar da shawarar a bai wa ’yan ƙasa, kungiyoyin farar hula, da ƙwararru damar duba da kuma miƙa ƙorafe-ƙorafe kan jerin sunayen waɗanda aka zaɓa.

Ya bayyana cewa irin waɗannan matakai za su ƙara wa jama’a kwarin gwiwa kuma su taimaka wajen tabbatar da sahihancin babban zaɓen 2027 wanda yanzu saura kwanaki 554, rahoton Premium Times.

INEC za ta fara rijistar masu kada kuri'a

A wani labarin, kun ji cewa hukumar zabe mai ta kasa watau INEC za ta fara rijistar masu kada kuri’a ta yanar gizo a ranar 18 ga watan Agusta, 2025.

Kara karanta wannan

Jerin manyan kujerun gwamnatin tarayya da Tinubu ya ba mutanen Kano a shekaru 2

INEC ta bayyana cewa rijistar za ta kasance wani mataki na farko a cikin shirye-shiryen da ake yi na gudanar da zaben gwamna a Jihar Anambra da zaben 2027.

A cewa INEC, ta kuduri aniyar karfafa hadin gwiwa da kungiyoyin fararen hula, jam’iyyu da kafafen yada labarai domin karfafa shiga harkokin zabe musamman ga matasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262