Sanata Barau Ya Tabo Kujerar Gwamna Abba a Gangamin Zaben Cike Gurbin Kano

Sanata Barau Ya Tabo Kujerar Gwamna Abba a Gangamin Zaben Cike Gurbin Kano

  • Jam'iyyar adawa a Kano watau APC ta shirya gangamin kamfe yayin da ake shirin zaben cike gurbi a Shanono da Bagwai da karashen na Ghari
  • Mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya jagoranci jiga-jigan APC zuwa wurin taron da ya mikawa yan takara tuta
  • Barau ya ce nasarar APC a wannan zaben cike gurbin zai kara tabbatar da shirinta na kwace kujerar gwamnan jihar Kano a zaben 2027

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Shirye-shiryen zaben cike gurbin dan Majalisar Dokokin Kano mai wakiltar Bagwai da Shanono, ya yi nisa yayin da APC ta shirya gangamin tallata dan takararta.

Mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya jagoranci kusoshin APC a gangamin neman goyon bayan al'ummar kananan hukumomin Bagwai da Shanono.

Sanata Barau ya jagoranci gangamin APC a Kano.
APC ta shirya gangami yayin da akw shirin zaben cike gurbi a Kano Hoto: @barauijibrin
Source: Twitter

Daily Trust ta rahoto cewa a ranar Asabar mai zuwa, 16 ga watan Agusta, 2025, hukumar INEC ta shirya zaben cike gurbi a mazabar, tare da karisa zabe a mazabar dan Majalisar jiha na Ghari (Kunchi).

Kara karanta wannan

Nyesom Wike ya sake samu yadda yake so a tsarin siyasar Rivers

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Barau ya jagoranci manyan APC

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar Bichi, da sauran manyan jiga-jigan APC.

Gangamin ya tara dubban jama’a da magoya bayan APC, inda shugabannin jam'iyya suka roki mazauna yankin da su fito kwansu da kwarkwata domin su dangwalawa APC.

A jawabinsa, Sanata Barau Jibrin ya ce zaben dan takarar APC, Ahmad Kadamu, zai ƙara tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta ci gaba da aiwatar da ayyuka a yankin.

Barau ya tabo batun zaben gwamna a 2027

"Ku fito ku kada wa APC kuri'unku a zaben cike gurbi, hakan zai zama farkon nasarorin da za mu samu a zaben gwamna da shugaban kasa mai zuwa a 2027."

Bayan gangamin kamfen, jerin gwanon motocin yakin neman zaben ya wuce zuwa Ghari, inda aka mika tutar jam’iyyar APC ga dan takarar zaben ƙarishe na kujerar.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sakawa kanwar Abdussamad BUA, ya ba ta mukami a gwamnatinsa

A nasa jawabin, Injiniya Bichi ya bayyana tabbacin cewa APC za ta lashe kujerun yan majalisar dokokin jiha, yana mai danganta wannan da irin ayyukan da jam’iyyar ta yi a matakin tarayya.

Gangamin APC a Kano.
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ya halarci kamfen APC a Kano Hoto: @Barauijibrin
Source: Twitter

Gwamnatin Tinubu za ta yi titi a Shanono/Bagwai

Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince a fitar da Naira biliyan 10 domin gina titin Bichi–Bagwai/Shanono–Gwarzo don sauƙaƙa jigilar amfanin gona.

Hon. Abubakar Bichi ya ƙara da cewa aikin yana cikin jerin alkawuran da aka yi wa yankin, kamar yadda Vanguard ta rahoto.

Alaka ta yi tsami tsakanin Ganduje da Barau?

A wani labarin, kun ji cewa alamu sun nuna cewa rikici ya fara raba kan jagororin jam'iyyar APC a jihar Kano da ke Arewa maso Yamma.

Wasu majiyoyi sun yi ikirarin cewa an fara zaman doya da manja tsakanin magoya bayan tsohon shugaban APC na kaaa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Sanata Barau Jibrin.

Rahotanni sun nuna cewa APC Kano ta kafa kwamitoci uku don shawo kan ‘ya’yan da suka ji an yi musu rashin adalci domin a daidaita matsalolin cikin gida.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262