Haɗaka: Babbar Matsala Ta Shiga ADC, Ɗan Majalisar Tarayya Ya Ƙalubalance Ta a Kotu

Haɗaka: Babbar Matsala Ta Shiga ADC, Ɗan Majalisar Tarayya Ya Ƙalubalance Ta a Kotu

  • Dan majalisa Leke Abejide ya soki dakatarwarsa daga jam’iyyar ADC, ya ce wasu "baƙi" suna kokarin kwace jam’iyyar da ya gina
  • Hon. Abejide ya ce an dade da korar shugaban ADC na Kogi, Kingsley Ogga, tun 2022, don haka ba shi da ikon dakatar da kowa
  • Ya bayyana cewa babu wata sahihiyar hadaka da wani ɓangare, ya ce hadakar ta mutu tun kafin a fara
  • Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Lokoja, Kogi - Dan majalisar wakilai na ADC tilo, Leke Abejide, ya yi magana bayan jam'iyyar ta dakatar da shi.

Hon. Abejide ya gagara yin shiru kan dakatarwarsa daga jam’iyyar, yana mai watsi da kowane irin hadaka.

Dan majalisa ya shigar da ADC kotu
Dan majalisa da ADC ta dakatar ya maka ta a kotu. Hoto: Hon. Leke Abejide.
Source: Facebook

Dan majalisa ya kalubalanci ADC da hadakarta

Hon. Abejide ya bayyana cewa ba zai yarda wasu mutane baki su kwace jam’iyyar da ya sha wahala wajen kafawa ba, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

Sule Lamido ya gano babbar matsalar 'yan hadaka, ya ba su.shawara kan 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abejide, wanda ke wakiltar mazabar Yagba a Majalisar Wakilai, ya bayyana haka ne yayin martani kan hadakar jam’iyyar ADC da kuma dakatarwar da Kwamitin Kogi ya yi masa.

Ya kalubalanci sahihancin dakatarwar, yana cewa shugabancin Kingsley Ogga ba ya kan doka, tunda an kore shi daga jam’iyyar tun 2022.

Ya nuna rashin jin daɗinsa da yadda ake tafiyar da jam’iyyar, yana cewa babu gaskiya da bin kundin tsarin mulki.

Abejide ya ce lamarin ya kai kotu, kuma zai nuna musu cewa ba wai bai san abin da yake yi ba ne, cewar The Guardian.

Ya kara da cewa ya zama abin mamaki yadda shi kaɗai dan majalisa daga jam’iyyar, wasu daga waje za su zo su kwace iko da jam’iyyar.

Dan majalisar ya ce yana ƙin kowace irin hadaka, yana mai cewa hakan kuskure ne da ba za a iya gyarawa ba.

“Babu hadaka saboda ba za ta yiwu ba. Ina da hurumin kalubalantar dukan matakan da suka dauka a kotu.

Kara karanta wannan

APC ta yi babban rashi, tsoho 'dan majalisar tarayya ya sauya sheka

“Hadakar me? Wannan hadaka ta mutu tun kafin ta fara. Mu je zabe mu ga wanda zai yi nasara. Kuskure an riga an tafka.

- In ji Abejide

Dakatarwar da ADC ta yi wa dan majalisarta ya bar baya da kura
Dan majalisa ya shirya maka ADC a kotu bayan dakatar dashi. Hoto: Hon. Leke Abejide.
Source: Twitter

Shawarar da Abejide ya ba ADC a Najeriya

Ya shawarci jagorancin Sanata David Mark da su canja salo, su nemi sabon tsari domin ADC ba za ta shiga cikin wannan tafiya ba.

Hon. Abejide ya bayyana cewa kundin tsarin jam’iyyar ya tanadi taron NEC kafin a samu sauyin shugabanci.

Jagoran ADC ya ce ya maka sabbin shugabannin da ba a san su ba a kotu, yana masu cewa ba su da matsayin doka a jam’iyyar.

Abejide ya bukaci a bi doka da tsarin kundin jam’iyyar domin a samu shugabanci na gaskiya da bin ƙa’ida.

Hon. Abejide ya yi wa ADC gori

Kun ji cewa jam'iyyar ADC na ci gaba da fuskantar matsala tun bayan haɗewa da jagororin adawar Najeriya.

Hon. Leke Abejide ya bayyana cewa babu inda wannan haɗaka za ta je domin ba za su iya ja da APC ba.

Ya yi barazanar cewa zai iya barin ADC da ya gina zuwa APC a duk lokacin da ya ga dama domin yana da ƴancin yin hakan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.