Adamu Garba Ya Tunawa Ƴan Najeriya Abin da Suka Manta tun Buhari na Raye a 2015

Adamu Garba Ya Tunawa Ƴan Najeriya Abin da Suka Manta tun Buhari na Raye a 2015

  • Adamu Garba II ya tuna yadda tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari ya karɓi Najeriya komai ya taɓarɓare a 2015
  • Matashin da ya nemi tikitin shugaban ƙasa ya ce APC ta yi matuƙar koƙari idan aka kwatanta da yadda ta gaji kasar nan a baya
  • Adamu ya ce Shugaba Buhari ya yi ƙoƙari matuka a zamanin mulkinsa, yanzu kuma Bola Ahmed Tinubu ya ɗora daga wurin da ya tsaya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Tsohon ɗan takara da ya nemi tikitin shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Adamu Garba ya bayyana cewa jam’iyyarsa ta karɓi Najeriya a birkice a 2015.

Idan baku manta ba bayan shekara 16 a mulki, jam’iyyar PDP ta sha kaye a hannun APC a babban zaben 2015.

Jigon APC, Adamu Garba.
Adamu Garba ya ce APC ta karɓi Najeriya a lokacin da babu wani abu da ke aiki Hoto: @AdamuGarba
Asali: Twitter

Premium Times ta rahoto cewa tsohon shugaban ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan ya sha kaye a hannun marigayi Muhammadu Buhari na APC.

Kara karanta wannan

'Yadda Buhari ya ki karbar kyautar jirgin sama da aka yi masa', Garba Shehu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Adamu ya tuna yadda Buhari ya karɓi Najeriya

Sai dai a yayin wata hira da tashar AIT a shirin Focus Nigeria, Adamu Garba, wanda ya nemi tikitin APC a 2023, ya ce jam’iyyarsu ta karɓi mulki ne a lokacin da Najeriya ta kai gargara.

“Duk wasu kayan aiki sun lalace a lokacin da APC ta zo. Muna da ginshikai huɗu, diflomasiyya, leƙen asiri, sojoji, da tattalin arziki, duka an yi kaca-kaca da su. Shi ya sa ƴan ta'adda suka mamaye ƙasarmu,” in ji shi.

Ya ce a lokacin da Boko Haram, 'yan fashi da makami, da kuma haramtacciyar ƙungiyar IPOB, wadda shugaban ta Nnamdi Kanu ke fuskantar shari’a kan zargin ta’addanci, sun mamaye Najeriya.

Wani namijin ƙoƙari Buhari ya yi a mulkinsa?

Duk da harin da 'yan fashin daji ke kaiwa jami'an tsaro a Arewacin ƙasar, Garba ya yabawa gwamnatin APC, yana cewa an riga an ci galaba kan Boko Haram da 'yan fashi.

Kara karanta wannan

Tinubu: An yi hasashen wanda zai zo na 1, na 2, na 3 da na 4 a zaɓen shugaban ƙasar 2027

“Yanzu da nake magana da ku, babu ko yanki guda a hannun Boko Haram. Ko ‘yan bindiga da suka ƙaru a wa’adin farko na Buhari, yanzu NSA ya yi nasarar kawar da su,” inji shi.

Adamu Garba ya yi fatali da duk wata ƙididdiga da ya kira ta bogi da ake nuna cewa tattalin arziki ya fi zama da gindinsa a lokacin mulkin PDP.

Marigari Buhari da Shugaba Bola Tinubu.
Adamu Garba ya ce APC ta karɓi mulkin Najeriya a 2015 lokacin da komai ya taɓarbare Hoto: @Mbuhari, @officialABAT
Asali: Facebook

Adamu Garba ya yabawa gwamnatin APC

“APC ta zo da gaskiya, ta fasa wannan ƙwallon da ake ganin yana ƙyalli amma babu komai a ciki. Don haka, dole ne a sake fasalin tattalin arziki.”
“Shugaba Buhari ya yi iya ƙoƙarinsa, amma bai samu damar kafa tushen tattalin arziki ba. Ya fi maida hankali ne kan harkar tsaro kuma ya yi kokari sosai.”
"Shugaba Bola Tinubu ya ce a'a, zai yi abin da kowa ke tsorata da shi. Zai cire tallafin mai gaba ɗaya, sannan ya saki Naira domin a san ainihin darajar ta."

Kara karanta wannan

Bayan tafiyar Atiku, an yi hasashen matsayi da PDP za ta ƙare a sakamakon zaɓen 2027

- Adamu Garba.

Shugaba Tinubu ya ja hankalin gwamnoni

A wani labarin, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci gwamnonin jam'iyyarsa ta APC da su zage damtse, sun dage wajen kawo ci gaba ga mutanen da ke ƙarƙashinsu.

Ya yi ikirarin cewa har yanzu ƴan Najeriya da dama ba su gamsu da yadda ake tafiyar da mulki da sanin amfanin romon dimokuraɗiyya ba.

Tinubu ya buƙaci shugabannin jam’iyya da ƴan siyasa da aka zaɓa da su sake kusantar jama’a tare da ƙara himma wajen kyautata rayuwar al’umma.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262