Tinubu: An Yi Hasashen Wanda Zai Zo na 1, na 2, na 3 da na 4 a Zaɓen Shugaban Ƙasar 2027
- Tsohon gwamnan jihar Ekiti kuma jigo a jam'iyyar PDP ya ce Shugaba Bola Tinubu ne zai lashe zaɓen shugaban kasa na shekarar 2027
- Ayo Fayose ya ce Bola Tinubu mutum ne mai wayau da dabara, kuma alamu sun nuna ya gama kama ƙuri'un Kudu, kaɗan yake buƙata a Arewa
- Fayose ya kuma yi hasashen cewa Peter Obi zai sake ba da mamaki, yana mai cewa shi zai zo na biyu a sakamakon ƙuri'un da za a kaɗa a 2027
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja - Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya yi hasashen cewa Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu zai lashe zaben 2027.
Fayose ya yi ikirarin cewa shugaban kasa ya gama kama Kudancin Najeriya, ƙuri'u kaɗan yake buƙata daga ƴan Arewa domin nasararsa ta tabbata.

Source: Twitter
Ayo Fayose ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TV a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli, 2025.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tsohon gwamnan ya yi hasashen cewa jam’iyyar PDP za ta kare a matsayi na hudu, jam'iyyar haɗaka watau ADC za ta zo na uku, yayin da Peter Obi zai zo na biyu a sakamakon zaɓen 2027.
Yadda Bola Tinubu zai ci zaɓen 2027
A rahoton Daily Trust, Fayose ya ce:
“Tinubu, tun kafin ya hau mulki ya haɗa APC, ya ɗaga darajarta, ya kayar da PDP a 2015. A 2023 ma, ba tare da haɗin gwiwar ‘yan adawa ba, ya tumurmusa kowa a zaɓe.
"Kuna tunanin mutumin da bai fiye magana ba, ba shi da wayo? Da ni ma ina da damar da yake da ita, da tuni na wuce haka. Mutumin nan ya gama kama Kudu, kaɗan yake buƙata a Arewa ya ci zaɓe.

Kara karanta wannan
Bayan tafiyar Atiku, an yi hasashen matsayi da PDP za ta ƙare a sakamakon zaɓen 2027
“Peter Obi zai ba da mamaki kowa ya san haka. Obi zai fi PDP samun ƙuri’u. PDP za ta zo ta hudu, ADC ta uku, APC ta farko, Obi zai zo na biyu, ka rubuta ka ajiye."

Source: Facebook
Ƴan Najeriya na kama maganar Fayose?
Dangane da batun ko ƴan Najeriya na kama maganarsa, tsohon gwamnan ya ce bai damu ba, wanda ya ga dama ya yarda, wanda bai ga dama ba kar ya yarda.
"Ba dole ne mutane su yarda da ni ba. Wannan ba damuwata ba ce. Ka san halin da jam’iyyarmu ke ciki a yau. Kuma addu’ata ita ce PDP ta zo ta hudu a zaɓe mai zuwa.”
PDP ta sauya wurin gudanar da taronta na ƙasa
A wani labarin, kun ji cewa jam’iyyar PDP ta sauya wuri da lokacin gudanar da babban taronta na ƙasa wanda za a zaɓi sababbin shugabanni.
PDP ta sanya ranar Asabar, 15 ga Nuwamba 2025 zuwa Lahadi, 16 ga Nuwamba, 2025 a matsayin ranakun da za ta gudanar da zaɓen shugabannin jam'iyya na ƙasa.
Sakataren yada labaran PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya sanar da cewa jam'iyyar ta sauya wurin gudanar da taron zuwa Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
