Ana Kewar Buhari, Tinubu da Manyan APC Za Su Yi Taron Farko na Maye Gurbin Ganduje
- Shugaba Bola Tinubu da Kashim Shettima za su jagoranci taron NEC na APC gobe Alhamis a birnin tarayya Abuja
- Ana sa ran girmama marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari wanda ya rasu yana da shekaru 82
- Taron zai tattauna batun shugabancin APC, bayan gayyatar wasu daga cikin mambobin kwamitin koli jam'iyyar
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
FCT, Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai jagoranci sauran fitattun jiga-jigan jam’iyya zuwa taron kwamitin zartarwa na jam'iyyar APC.
Za a gudanar da taron ne a gobe Alhamis 24 ga watan Yulin 2025 a birnin tarayya Abuja.

Source: Facebook
Taron APC: Ana sa ran karrama Buhari
Rahoton Vanguard ya ce cikin masu halartar taron har da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, tsohon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo.

Kara karanta wannan
2027: Gwamnan PDP, shugabanninta sun ba maraɗa kunya, sun goyi bayan Tinubu a fili
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Har ila yau, ana sa ran tsofaffin gwamnoni da mambobin kwamitin aiki na kasa da sauransu za su halarci taron.
Akwai alamun cewa za a gudanar da dan gajeren zama na karrama marigayi Shugaba Muhammadu Buhari a gobe, kasancewar wannan shi ne babban taron APC na farko tun bayan rasuwarsa.
Zaman yana cikin wasu muhimman abubuwan da za a tattauna da su a taron NEC da za a gudanar gobe a hedkwatar jam’iyyar ta kasa.
Taron da za a tattauna batun sabon shugaban jam’iyya mai cikakken iko, ana sa ran zai samu yawan halarta domin ba za a yi taron shugabanni na kasa ba kamar yadda aka saba, amma wasu daga cikin mambobin za su halarta.
Al’adar APC ita ce a gudanar da taron shugabanni na kasa kwana daya kafin NEC, amma yanzu za a bar wannan tsarin saboda matsalolin tsare-tsare, in ji majiyoyi daga jam’iyyar.

Source: Twitter
Wadanda ake sa ran za su halarci taron
Hakan ya sa za a fadada taron NEC na gobe domin ya kunshi wasu daga cikin mambobin kwamitin jam’iyyar da aka gayyata musamman, cewar Punch.
Dangane da kundin tsarin mulki na APC, mambobin NEC sun hada da shugabannin kasa da mataimaka, sakataren kasa, da shugabannin jam’iyya daga kowanne yanki na siyasa.
Haka kuma akwai lauyoyin jam’iyya, shugabannin kudi, shugabannin shiryawa, hulda da jama’a, jin dadin mambobi, da sauran shugabanni da mataimakansu.
Shugabannin mata da matasa, wakilan masu nakasa, shugabannin jihohi, shugabannin majalisa da wakilai daga kowanne yanki za su shiga wannan taro.
Mambobin kwamitin amintattu, tsofaffin shugabanni, ‘yan majalisa masu mulki da wadanda ba su da rinjaye, da wasu da za a kira ko nada su na daga cikin mahalarta.
Taron na NEC gobe na sa ran samun halartar wasu daga cikin mambobin kwamitin kolin jam’iyyar da aka gayyata zuwa wannan taro mai fadi.
Gwamna ya ce babu mai kayar da APC
Kun ji cewa gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru ya nuna goyon bayansa ga tazarcen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.
Gwamna Nwifuru ya bayyana cewa tazarcen Tinubu wani abu ne da Allah ya riga ya ƙaddara zai auku a Najeriya.
Gwamnan ya nuna cewa babu wata haɗakar ƴan adawa da za ta iya hana a sake zaɓen Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

