"An Karya Doka," Abin da Atiku Ya Yi Ana Jimamin Rasuwar Buhari ya Harzuƙa Ministan Tinubu

"An Karya Doka," Abin da Atiku Ya Yi Ana Jimamin Rasuwar Buhari ya Harzuƙa Ministan Tinubu

  • Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo (SAN) ya nuna takaicinsa kan yadda Atiku Abubakar ya saki takardar barin PDP ana tsakiyar jimami
  • Keyamo ya bayyana cewa hakan ya ƙara tabbatar da cewa ƙwaɗayin mulkin Atiku Abubakar ya zarce tausayi da jin ƙansa
  • Ministan ya kuma caccaki Atiku bisa amfani da tambarin gwamnatin tarayya a wasiƙar sauya shekarsa, ya ce hakan ya saɓa doka

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan fitar Atiku Abubakar daga PDP ana cikin jimamin rasuwar Muhammadu Buhari.

Keyamo ya ce bai kamata tsohon mataimakin shugaban ƙasa, ya fitar da wasikar ficewarsa daga PDP a daidai lokacin da ake alhinin rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Buhari ba.

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo.
Keyamo ya nuna ɓacin ransa kan fitar Atiku daga PDP ana tsakiyar jimamin rasuwar Buhari Hoto: @FKeyamo
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wani saƙo da ministan ya wallafa a shafinsa na X da aka fi sani da Twitter yau Laraba, 16 ga watan Yuli, 2025.

Kara karanta wannan

2027: A ƙarshe, Atiku Abubakar ya yi murabus daga jam'iyyar PDP mai adawa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Keyamo ya fusata da abin da Atiku ya yi

Keyamo ya ce ko da yake Atiku na da ƴancin sauya jam’iyya a kowane lokaci, amma fitar da wasikar a wannan mako na makokin Buhari ya nuna yana yunƙurin karkatar da hankulan jama’a zuwa ga kansa.

Ministan ya ce:

“A zahirin gaskiya, cikin mutuntawa, wannan abin da ka yi ya nuna cewa burinka na takarar shugabancin ƙasa ya rinjayi tausayi da jin ƙai.”

Keyamo ya ƙara da bayyana cewa duba da wasiƙar, Atiku ya shirya, ya buga, ya sa hannu, kuma ya miƙa wasikar fita daga PDP a washe garin ranar da aka sanar da rasuwar Buhari.

Ministan Tinubu ya gano kuskuren Atiku

Bugu da ƙari, Keyamo ya kalubalanci Atiku kan amfani da Tambarin Gwamnatin Tarayya, a cikin wasiƙarsa, yana mai cewa hakan ya sabawa doka.

“A bisa doka, ya sabawa sashe na 6 na dokar ‘Flag and Coat of Arms Act, Cap. F30, na dokokin Najeriya, 2004’ wanda ya haramta wa wanda ba ya rike da kujera a gwamnatin tarayya amfani da tambarin kasar," inji shi.

Kara karanta wannan

"Bai so": Buba Galadima ya fadi dalilin jawo Buhari cikin harkar siyasa

Keyamo ya ce amfani da tambarin yana iya rikita al’umma da yaudararsu su yi tunanin cewa Atiku na magana ne a madadin gwamnatin tarayya, alhali bai riƙe wani muƙami a gwamnati ba tun shekaru 18 da suka wuce.

Keyamo, Atiku Abubakar da marigayi Muhammadu Buhari.
Keyamo ya gano kuskuren da Atiku ya tafka a wasikar ficewarsa daga PDP Hoto: @Fkeyamo, @Atiku, @Mbuhari
Source: Twitter

An zargi Atiku da neman haifar da ruɗani

“Ka yi tunanin idan duk wasu tsofaffin jami’an gwamnati za su ci gaba da amfani da tambarin Najeriya a sako kansu na siyasa, ba makawa za a samu babban rikici da rudani.”

- Festus Keyamo, SAN.

Keyamo ya ce duba da matsayinsa a gwamnatin tarayya da kuma kasancewarsa lauya na ƙasa, nauyi ne a kansa ya kare kundin tsarin mulki da dokokin ƙasa.

Makinde ya yi martani kan sauya shekar Atiku

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana cewa tafiyar Atiku ba za ta yi wa PDP illa a siyasance ba.

Gwamna Makinde ya ce ficewar Atiku ba za ta rage karfin jam’iyyar PDP ko damar ta ba, yana mai cewa duk wanda zai kawo matsala gara ya tafi.

Ya ce babu abin damuwa dangane da jam’iyyar haɗaka watau ADC, a cewarsa ba wata barazana ba ce ga PDP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262