ADC: An Bayyana Wanda Zai Jagoranci Haɗakar Su Atiku zuwa Fadar Shugaban Kasa a 2027

ADC: An Bayyana Wanda Zai Jagoranci Haɗakar Su Atiku zuwa Fadar Shugaban Kasa a 2027

  • Uban jam'iyyar ADC kuma shugabanta na farko, Ralph Nwosu ya ce ƴan dawa sun shirya ƙwace mulki daga hannun APC a 2027
  • Nwosu ya bayyana David Mark, shugaban ADC na riko a matsayin mutumin da zai jagoranci ƴan adawa zuwa fadar shugaban ƙasa
  • A cewarsa, zai koma gefe tamkar mamba amma zai yi aiki tuƙuru domin ceto Najeriya daga mawuyacin halin da ta shiga

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Taohon shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark ya shirya jagorantar haɗakar ƴan dawa zuwa fadar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2027.

Ralph Nwosu, wanda ya kafa kuma ya kasance shugaban jam’iyyar ADC na farko ne ya bayyana hakan a taron da kungiyar haɗakar ta gudanar jiya Laraba.

Yan adawa sun hada kansu.
Yan adawa sun bayyana yaƙininsu kan sabon shugaban ADC na riko, David Mark Hoto: @Atiku
Source: Twitter

Ya ce David Mark, ne zai jagoranci manyan ƴan adawar ƙasar nan da nufin ƙwace mulki daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027, kamar yadda Daily Trust ta kawo.

Kara karanta wannan

Takarar shugaban ƙasa za ta tarwatsa Atiku, Obi da sauran ƴan haɗaka a ADC? An samu bayani

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

David Mark zai jagoranci ADC zuwa Aso Villa

Tun da farko ƙungiyar haɗakar ta naɗa David Mark da tsohon gwamnan jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin shugaba da sakatarensa na rikon ƙwarya.

Amma da yake jawabi a cibiyar taron Yar’Adua da ke Abuja yayin ƙaddamar da wannan jam'iyyar haɗaka watau ADC, Nwosu ya ce:

“Dukkanmu mun yanke shawarar yin murabus ne domin David Mark ya ja ragamar wannan jirgin ya kai mu fadar shugaban ƙasa.”

Nwosu ya bayyana Aregbesola, tsohon na hannun daman Tinubu a siyasa, wanda a yanzu suka samu saɓani, a matsayin mutum mai kyakkyawan tarihin ayyukan alheri.

ADC: 'Ƴan Najeriya na buƙatar sauyi a 2027'

“’Yan Najeriya na fatan samun sauyi, sun gaji da halin da ake ciki. Ina taya ku murna da kuma tabbatar muku da cewa tare da haɗin gwiwar mambobin NWC da NEC da za ku haɗu da su, ba za ku fuskanci wata matsala ba.”

Kara karanta wannan

ADC: Bayan hasashen El-Rufa'i, sabon rikici ya danno jam'iyyar hadakar adawa

Ya ƙara da cewa:

“Zan ci gaba da zama mamba kuma uba, aikina ba zai ƙare ba sai mun rera taken ƙasa a fadar shugaban ƙasa, wannan shi ne burinmu na gaskiya.
"Najeriya na cikin mawuyacin hali a ICU, kullum sai an rasa rayuka. Fata na shugabanni masu zuwa su ceto Najeriya daga wannan ƙangin, domin za mu iya.
“Za mu iya taimaka wa Mark da Aregbesola ta hanyar haɗa kanmu. Duk wanda ya soki abin da muka yi yau ba ɗan ADC ba ne.
Tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark.
Shirin jagororin adawa na kawo ƙarshen mulkin APC a 2027 ya kankama Hoto: @SenDavidMark
Source: Twitter

Jiga-jigan da suka halarci taron haɗakar ADC

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi, dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, rahoton Punch.

Sai kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, tsohon gwamnan Imo, Emeka Ihedioha da wasu fitattun ƴan siyasa.

Rotimi Amaechi ya fice daga jam'iyyar APC

Kara karanta wannan

Peter Obi ya mika wa 'yan adawa bukatar takara bayan samun sarauta a Pantami

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon Ministan sufuri kuma tsohon gwamnan jihar Ribas, Ritimi Amaechi ya fice daga APC a hukumance.

Amaechi ya yi ikirarin cewa Najeriya ta lalace a ƙarƙashin gwamnati mai ci, yana mai cewa lokaci ya yi da za a gyara ƙasar nan don dawo da ƙimarta.

A cewar tsohon ministan, gwamnatin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ba ta san halin da talakawa ke ciki ba, ta fi maida hankali kan neman tazarce.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262