Shirin 2027: Gwamnonin PDP da Wike Sun yi Zama don Dawo da Zaman Lafiya a Jam’iyyar

Shirin 2027: Gwamnonin PDP da Wike Sun yi Zama don Dawo da Zaman Lafiya a Jam’iyyar

  • Alamu sun nuna an samu sabuwar yarjejeniya tsakanin gwamnonin PDP da Wike a Legas kwanan nan
  • An tattauna rikicin Ribas da matsalolin shugabancin jam’iyya da duk wasu matsalolin da ake tsammanin za su kifar da jam’iyyar
  • Makinde ya ce dole ne a nemi mafita ta siyasa kafin 2027. A halin yanzu dai PDP na ci gaba da fuskantar koma-baya

Jihar Legas - Gabanin babban zaben shugaban kasa na 2027, wasu gwamnoni da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP sun gana da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike kan batun zaman lafiyar jam’iyya.

Wata majiya daga jam’iyyar ta shaidawa Sunday PUNCH cewa Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ne ya wakilci gwamnonin na PDP a taron da aka yi da Wike a Legas makon jiya.

A cewar majiyar, sun tattauna rikicin siyasa da ke tsakanin Wike da Gwamna Siminalayi Fubara wanda aka dakatar.

Yadda aka yi zama a PDP kan batun 2027
PDP na sake sabon shirin 2027 | Hoto: Nyesom Wike, Seyi Makinde
Source: Facebook

Hakazalika, sun yi batutuwa kan matsalolin shugabancin yankin Kudu masu Kudu da batun Sakatare na kasa wanda har yanzu ba a warware ba tun watan Disamban 2024.

Kara karanta wannan

'Dalilin da ya sa PDP ba ta ɗauki mataki kan Wike ba duk da zargin cin amana'

Rikicin PDP a wannan mulkin na Tinubu

Tun bayan zaben 2023, PDP na fama da rikicin cikin gida, inda yunkurin sasanci daga NWC, BOT, NEC da inuwar gwamnonin PDP ya gaza haifar da da mai ido ba, sai ma kara jefa jam’iyyar cikin rudani da rabuwar kai.

Rikicin ya haifar da bacin ran wasu jiga-jigai a jam’iyyar, har wasu suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

A ranar 23 ga Afrilu, Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori da tsohon gwamna Ifeanyi Okowa sun sauya sheka tare da wasu 'yan jam’iyyar zuwa APC, wanda hakan ya jefa PDP cikin matsanancin hali gabanin 2027.

Bayan ganawa da Wike a Legas

Majiyar ta ce bayan ganawar a Legas, Makinde ya yi alkawarin sanar da sauran gwamnoni, yayin da Wike zai sanar da magoya bayansa sakamakon ganawar.

Wike ya nuna bacin ransa kan yadda gamayyar gwamnonin ke daukar matakai ba tare da la'akari da dokokin jam’iyyar ta PDP ba.

Kara karanta wannan

Uwar Bari: Fubara zai kara zama da Wike a shirin sulhu a Rivers, APC da PDP sun magantu

Ya kuma jaddada cewa bai da niyyar barin PDP, sai dai ya bukaci da a sake duba wasu matsalolin da suka hada da rikicin Ribas, shugabancin Kudu maso Kudu da batun Sakatare na kasa domin a samu daidaito da hadin kai.

Makinde kan halin wasu mambobin PDP

Makinde ya koka kan yadda wasu manyan mambobin jam’iyyar ke nuna rashin mutunta gwamnoni, wanda ke kara dagula lamura.

Daga karshe sun amince cewa a soke duk wasu karar siyasa da ke gaban kotu sannan a nemi mafita ta siyasa.

Wani babban jigo daga kwamitin NWC ya tabbatar da aukuwar ganawar inda ya bayyana cewa tana da nufin dawo da hadin kai a jam’iyyar.

Yadda taro ya gudana

Shima Timothy Osadolor, mataimakin shugaban matasa na PDP, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta dawo da karfinta.

Ya ce:

“Wannan jam’iyya ce ta kowa da kowa. APC tamkar jirgi ne da ke cike da kaya; lokaci na nan da ba da jimawa ba za ta nutse.”

Atiku na jawo rikici a jam’iyyar, Jiga-jigan PDP

A bangare guda, wasu jiga-jigan jam’iyyar sun zargi tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da haddasa rikicin da PDP ke ciki.

Sun koka cewa, ya kamata fadi a fili cewa ba zai tsaya takara a 2027 ba. Sun bayyana cewa a baya Atiku ya fice daga PDP da wasu gwamnoni amma jam’iyyar ta tsira, don haka za su ci gaba da adawa da shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng