Sauya Sheka: Hadimin Buhari Ya ce za Su Yi Maraba da Kwankwaso a APC

Sauya Sheka: Hadimin Buhari Ya ce za Su Yi Maraba da Kwankwaso a APC

  • Magoya bayan jam’iyyu sun fara bayyana ra’ayoyinsu kan rade-radin da ke yawo cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso zai koma APC kafin zaɓen 2027
  • Hadimin Muhammadu Buhari ya ce za su marabci Kwankwaso idan ya dawo APC, yayin da wasu suka ce hakan zai janyo ce-ce-ku-ce a siyasar Kano
  • Tun a watan Janairu shugaban NNPP a Kano ya musanta zargin cewa Kwankwaso na shirin ficewa daga jam’iyyar zuwa APC mai mulki

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kano - Rahotanni na nuni da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin komawa APC.

Tun a farkon 2025 Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana cewa Rabiu Kwankwaso na neman hadin gwiwa da Shugaba Bola Tinubu domin karfafa gwamnatin Abba Kabir Yusuf.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta fadi ainihin abin da ya kai Bola Tinubu Faransa

Kwankwaso
Hadimin Buhari ya ce APC za ta yi maraba da Kwankwaso. Hoto: Hon. Saifullahi Hassan|Bashir Ahmad
Asali: Facebook

Hadimin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa za su yi maraba da Rabiu Kwankwaso idan ya sauya sheka zuwa APC.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai tun a watan Janairu, Daily Trust ta wallafa cewa jam’iyyar NNPP ta Kano ta musanta wadannan rade-radin.

'Za mu marabci Kwamkwaso a APC,' Bashir

Tsohon mai taimaka wa Shugaba Buhari, Bashir Ahmad, ya bayyana cewa APC za ta yi maraba da Kwankwaso idan har ya dawo.

Bashir ya ce:

“Za mu yi maraba da Sanata Kwankwaso da mutanensa cikin jam’iyyarmu ta APC.”

Sai dai magoya bayan jam’iyyun sun bayyana ra’ayoyi mabambanta, Ibrahim Dauda Isa ya yi zargi da cewa:

"Dama Kwankwaso yana aiki da APC tun 2023."

Othman Ya’u ya yi gargadin cewa:

"Dawowarsa APC zai lalata masa siyasa."

Japhet Danbaba Laya ta yi tambaya da cewa:

Kara karanta wannan

Abin ya fara damun Tinubu, an 'gano' shirinsa kan ƴan APC da ke son komawa SDP

"Ko wa zai kasance shugaban APC a Kano idan Kwankwaso ya dawo?"

Abu-Ammar Yareema ya yi hasashen cewa:

"Kwankwaso zai kwace jam’iyyar daga hannun Ganduje da magoya bayansa."
Kwankwaso
Jagoran NNPP a Najeriya, Sanata Kwankwaso. Hoto: Hon. Saifullahi Hassan
Asali: Facebook

Da gaske Kwankwaso zai koma APC?

Tun da aka fara rade radin a watan Janairu, shugaban NNPP na Kano, Hashim Dungurawa, ya bayyana cewa babu wani jigo da ke shirin komawa APC.

Ya ce:

“Gwamnanmu yana aiki, kuma shi ne gwamna mafi kwarewa a Najeriya yanzu. Me za mu ci idan mun bar NNPP muka koma APC?”

Dangane da kalaman Musa Iliyasu da ya ce Rabiu Kwankwaso zai koma APC, Dungurawa ya ce rade-radi ne kawai da ke neman tada zaune tsaye a siyasar jihar.

A yanzu haka dai ana sauraron ko NNPP za ta yi magana kan rade rade radin da ke yawo a kafafen sada zumunta game da sauya shekar Kwankwaso.

Shugabannin APC da NNPP sun koma SDP

Kara karanta wannan

Sanata Ndume na shirin ficewa daga APC ya haɗe da El Rufai a SDP? Ya yi bayani da bakinsa

A wani rahoton, kun ji cewa shugabannin jam'iyyun NNPP da APC sun sauya sheka zuwa SDP a jihar Kaduna.

Legit ta rahoto cewa dukkan shugabannin jam'iyyun sun koma SDP ne a mazabar Kargi da ke karamar hukumar Kubau ta jihar.

SDP na kara karfi a jihar Kaduna da wasu yankunan Arewacin Najeriya tun bayan komawar Malam Nasir El-Rufa'i jam'iyyar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng