"Mu ba Mabarata ba ne," Tsohon Ɗan Takara a Kano Ya Caccaki Ɗan Shugaba Tinubu

"Mu ba Mabarata ba ne," Tsohon Ɗan Takara a Kano Ya Caccaki Ɗan Shugaba Tinubu

  • Tsohon ɗan takarar Majalisa a Kano, Adnan Mukhtar TudunWada ya soki ziyarar da Seyi Tinubu ya kawo Arewa, ya ce wannan cin mutunci ne
  • Adnan ya bayyana cewa ɗan shugaban ƙasa bai isa ya yi wa sarakunan Kudu abin da ya yi wa na Arewa ba, yana mai cewa akwai raini a lamarin
  • Matashin ya shaida Legit Hausa cewa Arewa na bukatar a inganta ilimi, wutar lantarki, cibiyoyin fasaha da sauransu ba wai raba abinci ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Tsohon ɗan takarar Majalisar dokokin jihar Kano, Hon. Adnan Mukhtar TudunWada ya caccaki ziyarar da ɗan shugaban ƙasa, Seyi Tinubu ya kawo Arewa.

Hon. Adnan ya bayyana cewa abin da ɗan Bola Tinubu ya yi ba komai ba ne face cin mutunci da raina manyan mutane a Arewacin Najeriya.

Kara karanta wannan

'Me shirunsa ke nufi?' An taso Kwankwaso a gaba game da dokar ta ɓaci a Rivers

Adnan Mukhtar da Seyi Tinubu.
Hon. Adnan Mukhtar ya caccaki ziyarar ɗan shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu Hoto: Adnan Mukhtar TudunWada
Asali: Facebook

Adnan Mukhtar ya yi wannan zazzafan raddi ne a wata hira da ya yi da ɗaya daga cikin wakilan Legit Hausa ranar Laraba, 19 ga watan Maris, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matashin ɗan siyasa ya ce ƴan Arewa ba mabarata ba ne da ɗan shugaban kasar zai zo yana raba abinci, yana mai cewa hakan ba ƙaramin abin kunya ba ne.

Adnan ya caccaki ziyarar Seyi Tinubu

Ya kara da cewa abubuwan da Seyi Tinubu ya yi ya ƙara kashewa mahaifinsa kasuwa domin tuni suka fara wayar da kan jama'a kan su gujewa zaben waɗannan mutanen.

"Na ɗaya shi ba musulmi ba ne, ya zo ya yi buɗa baki da matasanmu, wani ma ya kira ni wai abin kunya ne ba a gayyace ni ba, to dan ban je na ci abinci da ɗan shugaban ƙasa ba sai menene? Ina da abincin a gidana.
"Ya zo ya raba mana abinci a leda, kamar almajirai kuma ka duba yadda ya je ya na gaisawa da sarakunanmu, ya na zama a kujera kamar gwamna, bayan ba rike yake da muƙami ba.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da batun Ribas, tsohon ɗan takara a Kano ya caccaki shugaban matasan PDP

"Amma aka ba shi kujerar gwamna a fadar sarkin Zazzau da sarkin Damaturu, ya zauna da takalmi yake shiga fada, wanda bai isa ya yi haka a Kudu ba."

- In ji Adnan.

Adnan Mukhtar.
Adnan ya jero abubuwan da Arewa suka fi bukata Hoto: Adnan Mukhtar TudunWada
Asali: Facebook

Seyi Tinubu ba zai yi haka a Kudu ba

Tsohon ɗan takarar Majalisar Kano ya ƙara da cewa Seyi Tinubu bai isa ya yi wa sarakunan Kudu abin da ya yi wa sarakunan Arewa ba.

"Bai isa ya shiga fadar Ooni na Ife da takalmi ba, bai isa ya ba shi hannu ba. Bai isa ya je fadar Alaafin na Oyo ya ba shi hannu ko ya shiga da takalmi ba, bai isa ya yi haka a fadar Oba na Legas ba.
"Wannan rashin mutunci ne (abin da ya yi a Arewa) kuma wannan raini ne," in ji Hon. Adnan Mukhtar.

Abubuwan da mutanen Arewa ke bukata

Adnan ya ƙara da cewa abin da al'ummar Arewa ke bukata shi ne a inganta ilimi, samar da cibiyoyin fasahar zamani (ICT), wutar lantarki, ƙarin makarantu da sauran abubuwan ci gaba.

Kara karanta wannan

Ba jira: Ministan Tsaro, Matawalle ya fadi shirin sojoji kan dokar ta baci a Rivers

Ya ce wannan shi ne abin da ƴan Arewa ke buƙata ba abincin da ɗan shugaban ƙasa ya raba ba, wanda iyakarshi rana guda.

Adnan ya soki shugaban matasan PDP

A wani labarin, kun ji cewa Hon. Adnan ya soki shugaban matasan PDP na ƙasa, Muhammad Kadade, ya ce ya kamata a tashi tsaye.

Tsohon ɗan takarar ya bayyana cewa Kadade ya gaza jagorantar matasa yadda ya kamata, ya koma ɗaukar hotuna da manyan mutane.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng