Kaduna: Ɗan PDP Ya Aikawa Sanatansa Sako Ya Hana Dakatar da Fubara a Majalisa

Kaduna: Ɗan PDP Ya Aikawa Sanatansa Sako Ya Hana Dakatar da Fubara a Majalisa

  • Wani matashi dan jam'iyyar PDP a Kaduna, Aliyu Kwarbai ya tura sako ga Sanata Ibrahim Khalid Soba kan dokar ta-ɓaci a Rivers
  • Kwarbai ya roki sanatan ka da ya goyi bayan cire Gwamna Simi Fubara daga kujera, yana cewa hakan zai bar baya da kura a jihar
  • 'Dan siyasar ya bayyana cewa ya taimaka wurin yakin zaben sanatan a 2023, amma bai taba neman wani abu a wajensa ba
  • Ya roƙi Soba da ya tsaya tsayin daka wajen kare dimukradiyya da adalci, yana cewa hakan ne abin da ya dace da shugaba na gari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kaduna - Wani daga cikin matasan 'yan siyasa a jam'iyyar PDP a jihar Kaduna ya tura sako ga sanatansa kan dokar ta-ɓaci a Rivers.

Kara karanta wannan

Fubara: Atiku, El Rufai, Obi da mutanen Buhari sun tunkari Tinubu da murya daya

Matashin mai suna Aliyu A. Kwarbai ya tura sakon ne da yake rokon Sanata Ibrahim Khalid Soba ya ki amincewa da tabbatar da dokar.

Dan PDP ya roki sanatansa kan cire Gwamna Fubara
'Dan PDP a Kaduna ya roki sanatansa ya hana dakatar da Gwamna Fubara a majalisa. Hoto: @AliyuKwarbai, Sir Siminalayi Fubara.
Asali: Twitter

Rivers: 'Dan PDP ya roki Sanatansa daga Kaduna

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Aliyu Kwarbai ya wallafa a shafin X a yau Alhamis 20 ga watan Maris, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin sanarwar, matashin ya ce ya tura sakon ne ga Sanata Ibrahim Khalid Soba da ke wakiltar Kaduna ta Arewa a Majalisar Dattawa.

Kwarbai wanda ya so tsayawa takarar shugaban karamar hukumar Zariya, ya roki Sanatan ka da ya amince da bukatar shugaban kasa.

An bukaci majalisa ta yi na'am a dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara daga kujerarsa a jihar.

Matashin ya ce hakan zai kare dimukradiyya da kuma wasu abubuwa da ka iya biyo bayan amincewa da cire gwamnan.

A cikin rubutunsa ya ce:

"Ina kwana, jajirtaccen sanatan yankina, sunana Aliyu Kwarbai, mun yi magana na karshe ne tun ana saura mako daya a yi zaben ka.

Kara karanta wannan

Rivers: Atiku ya sauya salo, ya roƙi ƴan Najeriya bayan Tinubu ya sanya dokar ta ɓaci

"A matsayina na ɗan a mutun PDP, na ba da gudunmawa wurin yakin neman zabenka kuma ban taba neman wani taimako a wurinka ba saboda na san halin da ake ciki.
"Amma a yau zan nema, duk yadda za a yi ka da ka goyi bayan cire Gwamna Fubara a Rivers, ka kare dimukradiyya, Nagode sanatana."
Wani ɗan PDP ya roki Sanatansa ka da ya bari a cire Fubara daga kujerarsa
Wani ɗan PDP a Kaduna ya roki Sanata Ibrahim Khalid Soba ka da ya amince da cire Gwamna Siminalayi Fubara daga kujerarsa. Hoto: Sir Siminalayi Fubara, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Twitter

Martanin wasu masu amfani da kafar X

Wasu masu ta'ammali da shafin X sun bayyana ra'ayinsu kan sakon matashin ga Sanatan da ke wakiltarsa a mazabar Kaduna ta Arewa.

@Tazaya_:

"Har yanzu shi yake wakiltar mazabar Kaduna ta Arewa?"

@hithertOO:

"Wannan ai dan zaman benci ne, abin da su ke so kawai zai yi."

@kabir_baba:

"Mai girma Sanata ba."

@salisuahmed51:

"Kuma ba zai taba mayar da martani ba."

@GodwinC15:

"Dalilin haka, ka sa na fara bibiyar shafinka."

Atiku ya caccaki Tinubu kan sanya dokar ta-ɓaci

Mun ba ku labarin cewa tsohon dan takarar shugaban kasa a PDP, Atiku Abubakar, ya bukaci 'yan Najeriya su tashi tsaye su kare dimokuradiyya daga dokar ta-baci a Rivers.

Kara karanta wannan

Gwamna ya maida martanin barazanar dakatar da shi kamar yadda aka yi a Ribas

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa tilas ne a hana wannan yunkuri na kifar da gwamnatin da aka zaba ta hanyar doka marar dalili.

Atiku ya fadi hakan ne a Abuja yayin wani taron manema labarai na wasu shugabannin siyasa da ke nuna damuwa kan halin da ake ciki a jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng