Jerin Majalisun Dokoki na Jihohi 6 da Aka Sha Fama da Rikicin Shugabanci a Najeriya
A makon jiya ne rikicin da ya ɓarke a Majalisar dokokin jihar Legas ya buɗe sabon shafi, inda jami'an tsaro suka mamaye zauren Majalisar ranar Litinin.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Rikicin dai ya ƙara ƙamari a lokacin da dakarun suka rufe ofisoshin kakakin majalisar dokokin, Hon. Mojisola Meranda, mataimakinta da magatakarda.

Asali: Twitter
Duk wannan rigima da ke faruwa ta samo asali ne daga tsige tsohon kakakin majalisar, Hon. Mudashiru Obasa, kamar yadda Daily Trust ta kawo.
Tsige Obasa ya raba kawunan shugabannin APC a jihar Legas, wasu na ganin ƴan majalisar sun yi gaban kansu wajen canza shugabanci ba tare da tuntuba ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Legit Hausa ta tattaro maku rigingimun shugabanci da suka faru a wasu Majalisun dokoki na jihohin ƙasar nan, ga su kamar haka:
1. Majalisar dokokin jihar Legas
Rigima ta ƙara ɗaukar zafi a Majalisar dokokin jihar Lagos lokacin da jami’an DSS suka mamaye zauren bisa umarnin magatakarda, rahoton This Day.
A wannan rana, 'yan majalisa sun kutsa kai cikin zauren majalisar da karfi, inda suka bayyana goyon bayansu ga sabuwar kakaki, Hon. Mojisola Meranda.
Majalisar GAC, wanda shi ne lamba ɗaya wajen yanke shawara a APC ta Legas, ya shirya ganawa da shugaba Bola Tinubu domin tattaunawa kan rikicin da ke faruwa a majalisar.

Asali: Twitter
An ruwaito cewa rikicin ya kara kamari sakamakon yunkurin tsohon kakakin majalisa, Hon. Mudashiru Obasa, na komawa kan mukaminsa.
Obasa, wanda aka tsige daga mukaminsa a ranar 13 ga Janairu, 2025, ya kai majalisar da sabuwar kakakin gaban babbar botun jihar Legas da ke Ikeja.
Ya kalubalanci matakin cire shi daga muƙaminsa, yana mai cewa an tsige shi ne ba bisa ka’ida ba, duba da cewa majalisar tana cikin hutun aiki a lokacin da hakan ta faru.

Kara karanta wannan
Mai alfarma sarkin musulmi ya aika saƙo ga malamai ana shirin fara azumin Ramadan
2. Majalisar dokokin jihar Ribas
A watan Disamba 2023, aka fara zargin cewa mambobi 27 na Majalisar dokokin Ribas sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, a lokacin da rikicin siyasa ya tsananta a jihar.
Wadannan ‘yan majalisa, karkashin jagorancin Rt. Hon. Martins Amaewhule, suna da goyon bayan tsohon gwamnan jihar, kuma ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike.

Asali: Facebook
A gefe guda, wani bangare na majalisar da ke karkashin jagorancin Victor Oko Jumbo wanda ke da mambobi biyar, yana goyon bayan Gwamna Simi Fubara.
Wannan rikici na ci gaba da jefa siyasar jihar Ribas cikin rudani, lamarin da ya kai shigar ƙararraki gaban kotu, kamar yadda Ripples Nigeria ta kawo.
3. Majalisar dokokin jihar Ogun
A watan Janairu 2024, ƴan majalisar dokokin Jihar Ogun 18 suka tsige Olakunle Oluomo daga mukamin kakakin majalisar.
Daily Trust ta tattaro cewa bayan tsige shi, majalisar ta zabi Hon. Oludaisi Elemide, wanda ke wakiltar mazabar Odeda, a matsayin sabon kakaki.

Asali: Facebook
Rahotanni sun nuna cewa lokacin da aka tsige shi, Oluomo ya tafi cibiyar al’adu ta June 12 a Kuto, Abeokuta, domin halartar bikin rantsar da alkalai.
Gwamnan jihar, Dapo Abiodun ya danganta tsige Oluomo da rikicin cikin gida da ya daɗe yana faruwa a majalisar, wanda ya kara kamari duk da yunkurin sasanta bangarorin da suka samu sabani.
4. Majalisar dokokin jihar Ondo
A ranar 2 ga Yuni, 2023, jami’an tsaro suka rufe Majalisar dokokin jihar Ondo sakamakon wani yunkuri na tsige kakakin majalisar, Bamidele Oloyelogun.
Wannan mataki ya biyo bayan wata wasikar murabus da ake zargin an rubuta a madadin Hon. Oloyelogun.

Asali: Facebook
Rahotanni sun bayyana cewa an rubuta wasikar ne cikin gaggawa don gujewa tsige shi, kwanaki kadan kafin karewar wa’adin majalisa ta 9 da yake jagoranta.
Jami’an tsaro sun toshe dukkanin kofofin shiga majalisar, lamarin da ya dakatar da duk wani aiki, komai ya tsaya cak.

Kara karanta wannan
Gwamna Abba zai jiƙa mutanen Kano da ayyukan alheri, ya ware sama da Naira biliyan 30
A ranar 4 ga Yuni, 2023, Olamide Oladiji ya zama sabon kakakin majalisar dokokin jihar Ondo, kamar yadda Daily Post ta tattaro.
5. Majalisar dokokin jihar Nasarawa
A 2023, rikici mai cike da rudani ya barke a Majalisar dokokin jihar Nasarawa, wanda ya kai ga darewar Majalisar gida biyu, kowane na ikirarin shugabanci.
An zabi Hon. Daniel Ogazi da Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dukkansu ‘yan jam’iyyar APC a matsayin shugabannin majalisar a lokuta daban-daban, cewar rahoton Gazettengr.

Asali: Facebook
Abdullahi, wanda shi ne tsohon kakakin majalisar, kuma wanda ke neman wa’adi na uku, an sake zabarsa ne a wani zama da aka yi a ma’aikatar ƙananan hukumomi.
A daya bangaren kamar yadda Channels tv ta kawo labari cewa Hon. Ogazi ya bayyana a matsayin kakakin majalisar a lokacin wani zama da mambobi suka gudanar a harabar majalisar da ke Lafia.
6. Majalisar dokokin jihar Benuwai

Kara karanta wannan
'Yan Majalisa 27 sun tattara kayansu sun fice daga jam'iyyar APC? an samu bayanai
A 2018, ‘yan majalisar dokokin Benuwai sun dakatar da kakakin majalisar da suka tsige, Terkimbi Ikyange, na tsawon watanni shida bisa zargin rashin ɗa'a.
‘Yan majalisar sun yanke wannan hukunci ne a zaman da suka yi a gidan gwamnati da ke Makurdi, saboda ‘yan sanda sun kulle kofar shiga zauren majalisar kan rikicin da ke faruwa.

Asali: Facebook
Wasu daga cikin ‘yan majalisar sun yi kokarin haura katangar majalisar don su shiga harabar ginin, amma sai suka tarar da ɗakin da suke zama a kulle.
Bayan sun kasa gudanar da zamansu a zauren majalisar, sai suka koma gidan gwamnati, suka ci gaba da harkokinsu har suka dakatar da kakakin, rahoton Channels tv.
Kakakin majalisar Legas ta yi murabus?
A wani rahoton, kun ji cewa kakakin Majalisar dokokin jihar Legas, Hon. Majisola Meranda ta ƙaryata labarin da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta cewa ta yi murabus.
Hon. Meranda, mace ta farko da Allah ya ba matsayin shugabar Majalisar dokokin Legas a tarihi, ta ce tana nan daram a kujerarta.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng