APC Za Ta Kafa Gwamnatin Basaja a Kano, Za a Bi Diddigin Ayyukan Abba Gida Gida
- Jam’iyyar APC ta sanar da shirinta na kafa gwamnatin basaja a Kano domin bin diddigin ayyukan gwamnatin Abba Kabir Yusuf
- Kungiyar APC za ta tura wakilanta zuwa ma’aikatun gwamnati domin bibiyar ayyuka, sannan su fitar da rahotannin adawa
- Shugaban kungiyar, Alhaji Usman, ya ce za su sanar da jama’a cikakken shirin nan gaba, domin tabbatar da adalci a mulkin Kano
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Kano - Jam’iyyar APC ta bayyana shirin kafa gwamnatin basaja a Kano domin sa ido kan tafiyar da mulkin Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP.
Shugaban kungiyar masu kishin APC da ke cikin jam'iyyar a Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya bayyana haka a wani taro da kungiyar ta gudanar don sabunta shirye-shiryenta.

Asali: Twitter
'Yan APC za su kafa gwamnatin basaja a Kano
A cewar Alhaji Usman, gwamnatin basaja za ta sanya ido kan ma’aikatun gwamnati, domin ta fitar da rahotannin suka masu ma'ana, inji rahoton The Nation.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaban kungiyar ya ce wannan tsari ana yin irin sa a Birtaniya, inda ‘yan adawa ke nada ministoci na basaja don duba ayyukan gwamnatin da ke mulki.
Kungiyar ta ce za ta kawo irin wannan tsarin ne da nufin tabbatar da cewa an gudanar da mulki bisa tsari da bin ka’idojin da suka dacewa a Kano.
Alhaji Usman Alhaji ya ce APC za ta tura wakilanta zuwa dukkanin hukumomin gwamnati a Kano domin bin diddigin ayyukan da ake yi.
APC na zargin Abba da rashin iya mulki
Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba za su gudanar da taron manema labarai don sanar da jama’a cikakken shirin.
A cewarsa, hakan zai bai wa jama’a damar sanin yadda ake tafiyar da ayyukan gwamnati da kuma yiwuwar yin gyara.
Jam’iyyar APC ta dade tana sukar salon da Abba ke amfani da shi wajen tafiyar da mulkin Kano, inda take zargin cewa ba a tafiya da Kano bisa turba madaidaiciya.
Yanzu dai ana jiran matakin da gwamnatin Kano za ta dauka dangane da wannan sabon yunkuri na jam’iyyar adawa.
Kusoshin NNPP sun koma APC a Kano
A wani labarin, mun ruwaito cewa, Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya tarbi gungun 'yan NNPP da suka sauya sheka zuwa APC a Kano.
Wasu daga cikin wadanda suka sauya shekar sun ce sun gaji da salon shugabancin Kwankwasiyya, wanda suka bayyana a matsayin na danniya.
Asali: Legit.ng