Zaben 2027: Gwamna Ya Fadi Fargabar APC kan Shirin Hadakar 'Yan Adawa

Zaben 2027: Gwamna Ya Fadi Fargabar APC kan Shirin Hadakar 'Yan Adawa

  • Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya taɓo batun yiwuwar yin haɗakar jam'iyyun adawa domin tunkarar zaɓen 2027
  • Hope Uzodimma ya bayyana cewa jam'iyyar APC ba ta da wata fargaba kan ƙulle-ƙullen da ƴan adawan suke yi domin karbar iko
  • Shugaban gwamnonin APC ya ce jam'iyyar ba ta tsoron shiga zaɓe kuma ƴan Najeriya ne za su yi mata hukunci a takarar 2027

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Gwamnan jihar Imo kuma shugaban gwamnonin jam’iyyar APC, Sanata Hope Uzodimma, ya yi magana kan shirin haɗaka na ƴan adawa.

Gwamna Uzodimma ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba ta jin tsoron tarukan da manyan jam’iyyun adawa ke yi a ƙoƙarinsu na shirin zaɓen 2027.

Uzodimma ya ce APC ba ta fargaba kan 'yan adawa
Hope Uzodimma ya ce 'yan Najeriya ne za su yi wa APC alkalanci a 2027 Hoto: Hope Uzodimma
Asali: Twitter

Uzodimma ya yi wannan bayanin ne a ranar Laraba a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Abuja, cewar rahoton jaridar Tribune.

Kara karanta wannan

Jigon APC ya dawo daga rakiyar Tinubu, ya fadi babbar nadamar da ya yi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya yi magana ne yayin da kwamitin zartarwa na jam’iyyar APC na ƙasa (NWC) ya rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya da kamfanin Tunmef Global Limited don fara aikin rajistar mambobin jam'iyyar.

Wannan mataki zai bai wa jam’iyyar damar samun cikakkun bayanai game da mambobinta.

Ƴan adawa sun fara yin taro

Rahotanni sun nuna cewa wasu manyan shugabannin jam’iyyun adawa na tattaunawa kan yiwuwar yin haɗaka domin fuskantar zaɓen 2027.

A ranar Litinin, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya jagoranci tsofaffin gwamnonin jihar Cross River da Sokoto, Lyel Imoke da Aminu Tambuwal, zuwa wajen Olusegun Obasanjo a birnin Abeokuta na jihar Ogun.

Haka nan, tsohon gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya hadu da tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, a wata ganawa da ake zaton tana da alaƙa da zaɓen 2027.

Wace fargaba APC ke da ita kan zaɓen 2027?

Kara karanta wannan

Alamu sun ƙara karfi, gwamna na shirin neman takarar shugaban ƙasa a 2027

Sai dai Uzodimma ya jaddada cewa jam’iyyar APC ba ta da wata fargaba, yana mai cewa ƴan Najeriya ne za su yankewa jam'iyyar hukunci a zaɓe mai zuwa.

"Ba mu jin tsoron abin da ƴan adawa za su ce. Aikinmu shi ne mu shirya jam’iyyarmu yadda za a girmama ta a duniya. Muna jiran zuwan zaɓe, kuma APC ba jam’iyya ba ce da ke gudun shiga zaɓe."
"Babu wata dimokuradiyya a duniya da ba a yin adawa. Ƴan Najeriya ne za su yanke hukunci wajen zaɓar wanda suke so."

- Gwamna Hope Uzodimma

Shugaban APC ya yabi Tinubu

A yayin bikin rattaɓa hannu kan yarjejeniyar rajistar mambobin, shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya godewa shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa amincewarsa da shirin.

"A matsayina na shugaban jam’iyya, muna ci gaba da kafa tarihi a siyasarmu."
"Ina son na godewa shugaban ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, bisa amincewarsa da wannan tsarin na yin rajistar. Wannan shiri an daɗe ana tunaninsa, amma ba a aiwatar da shi ba sai yanzu."

Kara karanta wannan

Zance ya kare, kotun ƙoli ta yanke hukunci kan bukatar tsige 'yan Majalisa 27

- Abdullahi Umar Ganduje

Ƴan APC sun yi wa Tinubu alƙawari

A wani labarin kuma, kun ji cewa wata ƙungiyar jam'iyyar APC ta yi wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu alƙawarin ruwan ƙuri'u a zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta ɗaukarwa shugaban ƙasa alƙawarin samar masa da ƙuri'u miliyan huɗu a zaɓen 2027, saboda gamsuwar da ta yi da kamun ludayin mulkinsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng