"An Zuba wa INEC Ido Ta na Sha'aninta," Makusancin Kwankwaso Ya Dira kan Hukumar Zabe

"An Zuba wa INEC Ido Ta na Sha'aninta," Makusancin Kwankwaso Ya Dira kan Hukumar Zabe

  • Tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa, ya ce dole ne a hukunta INEC da jami’an gwamnati kan kura-kuran zaɓe da ake maimaita wa
  • Bishof Isaac Idahosa ya kuma ba hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa shawarar yadda za a kauce wa aikata magaudi a zabukan Najeriya
  • A kan rikicin NNPP, makusancin na Sanata Kwankwaso ya jaddada cewa babu wani tsagi a jam'iyyarsu, domin tuni aka kori masu son kawo rikici

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Lagos - Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam'iyyar NNPP a zaɓen 2023, Bishof Isaac Idahosa, ya ce dole ne a hukunta hukumar zaɓe ta kasa (INEC).

Baya ga hukumar INEC, Bishof Idahosa na son a kara da hukunta jami'an gwamnati saboda kura-kuran da suka faru a zaɓe.

Kara karanta wannan

An taso gwamna a gaba kan nada tsohon shugaban APC ya jagoranci hukumar zabe

Kwankwaso
Dan takarar mataimakin shugaban kasa ya ce har yanzu ya na tare da Kwankwaso Hoto: Sunusi Bature D-Tofa
Asali: Facebook

A hirar da ya yi da Channels Televsion, tsohon ɗan takarar a karkashin NNPP, ya koka kan yadda ba a duba kura-kuran da INEC ke tafkawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Ba a hukunta hukumar INEC,” Idahosa

Bishof Idahosa ya bayyana cewa akwai kurakurai a yadda ake barin hukumar zaɓe ta INEC tana aikinta ba tare da kulawa ba.

Ya ce:

“Ba mu hukunta kowa a kan abin da ya aikata; babu hukunci, don haka ana ci gaba da maimaitawa.”

Ya ƙara da cewa:

“INEC na aikata kura-kurai, amma ba wanda ke sa ido a kanta, don haka su kan ci gaba da maimaita kurakuran.

Bishof Idahosa ya ba INEC shawara

Jagora a jam'iyyar NNPP ya bukaci a daidaita tsarin zaɓe ta yadda za a gudanar da duk zaɓukan a rana guda domin tabbatar da gaskiya da adalci.

Ya ce:

“Ina son bayar da shawarar a gudanar da dukkan zaɓuka a rana guda. Wannan zai taimaka matuƙa wajen hana maguɗi – zaɓen shugaban ƙasa, sanata, da gwamna duk a rana guda. Zai rage kashe kuɗi kuma a samu sakamako mai kyau.

Kara karanta wannan

Ana zargin gwamna ya ɗirkawa fitacciyar jaruma ciki a Najeriya, gaskiya ta bayyana

Amma idan an raba su mako ɗaya ko biyu bayan zaɓen shugaban ƙasa, ana iya yin maguɗi ko amfani da tasirin wani zaɓe a wani.”

‘Har yanzu ina kusa da Kwankwaso’ – Idahosa

Bishof Idahosa ya bayyana cewa har yanzu ya na da da kusanci da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kuma har yanzu shi ne jagora a NNPP.

Ya ce:

“Da farko, har yanzu ina kusa da shugabana. Ya zo nan makon da ya gabata – ranar 8 ga Fabrairu lokacin da nake bikin cikar shekaru 60.
Don haka har yanzu muna da kusanci, muna da kyakkyawar alaƙa. Babu wata matsala a jam’iyyarmu, har yanzu shi ne jagoranmu na ƙasa, Mai girma Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso.”
“Ba mu da ɓangarori daban-daban; tuni an kore su daga jam’iyya. Babu wata bukata ta yayata maganar baraka a jam’iyyarmu – muna da jam’iyya guda da ke ƙarƙashin jagorancin Mai girma Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso.”

Kara karanta wannan

Gwamnatin jihar Kano ta runtuma kora a ma'aikatar shari'a, an samu karin bayani

Yadda Kwankwaso ya zabi Idahosa a 2023

A baya, mun wallafa cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa ya yi bincike mai zurfi kafin ya zaɓi abokin takararsa.

A yayin kaddamar da Bishof Isaac Idahosa a matsayin mataimakin takararsa a babban zaɓen 2023, Sanata Kwankwaso ya bayyana cewa ya duba sama da mutane 20 kafin yanke shawara.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.