2027: Tsofaffin Gwamnnonin PDP 5 da Za Su Iya Goyon Bayan Tinubu Idan Ya Nemi Tazarce

2027: Tsofaffin Gwamnnonin PDP 5 da Za Su Iya Goyon Bayan Tinubu Idan Ya Nemi Tazarce

  • Yayinda Najeriya ke ci gaba da gudanar da dimokuradiyya ba tare da tangarda ba, kasar na tunkarar babban zaben shekarar 2027
  • Ana ci gaba da tattaunawa game da zaben 2027, zabe na takwas tun bayan dawowar Najeriya kan turbar dimokuradiyya a 1999
  • Legit Hausa ta jero wasu tsofaffin gwamnonin PDP da za su iya goyon bayan shugaba Bola Tinubu idan ya nemi tazarce a mulki

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Akwai yiwuwar cewar shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu zai nemi tazarce idan wa'adinsa ya kare a shekarar 2027.

Tun da ya shiga siyasa, an ce shugaba Bola Ahmed Tinubu bai taba hada kai da jam’iyyar adawa ta PDP ba.

An hasasho tsofaffin gwamnonin PDP da za su iya goyon bayan Tinubu a 2027
Wike, Akume da jerin wasu tsofaffin gwamnonin PDP da za su iya tallata Tinubu a 2027. Hoto: @officialSKSM, @GovWike
Asali: Twitter

Sai dai kuma babban jigo a jam’iyyar ta APC na iya samun goyon bayan wasu ’yan siyasa da suka jagoranci jihohin Najeriya a karkashin PDP.

Kara karanta wannan

APC ta yi kaca kaca da Atiku Abubakar, ta fadi wanda ke haddasa rikici a PDP

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit.ng Hausa ta jera wadannan mutanen.

1. George Akume

Rahotanni sun bayyana cewa Akume ya rike matsayin gwamnan jihar Benue na wa'adi biyu, daga 1999 zuwa 2007, a karkashin PDP.

Shi ne ministan ayyukan na musamman da harkokin gwamnati daga 2019 zuwa 2023 a zamanin shugaban Muhammadu Buhari.

Akume ya kasance sanata daga 2007 zuwa 2019 kuma shugaban marasa rinjaye na majalisar dattijai daga 2011 zuwa 2015.

A halin yanzu, Akume shi ne sakataren gwamnatin tarayya (SGF) kuma yana iya goyon bayan sake zaben Tinubu a 2027.

2. Chimaroke Nnamani

Nnamani ya kasance likita kuma dan siyasa, wanda ya zama gwamnan jihar Enugu daga 1999 zuwa 2007 a karkashin jam'iyyar PDP.

Chimaroke Nnamani ya zama sanatan yankin Enugu ta Gabas daga 2007 zuwa 2011 sannan an sake zabenshi a 2019.

The Punch ta ruwaito Nnamani yana cewa ya goyi bayan Tinubu a 2023 saboda rashin adalci ya fuskanta daga PDP.

Kara karanta wannan

'Buhari ya nuna rashin gamsuwa da mulkin Bola Tinubu,' PDP ta tono magana

Akwai yiwuwar cewar tsohon gwamnan na Enugu zai goyi bayan Tinubu a 2027 musamman ganin yadda yake kare shugaban kasar a fili.

3. Samuel Ortom

Ortom ya zama ministan harkokin kasuwanci da zuba jari a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan.

Ya zama gwamnan Benue a APC a shekarar 2015, amma daga baya ya koma PDP, sannan aka sake zabe shi a 2019.

Mulkin Ortom ya kare a 2023. A Janairu 2024, Ortom ya ce tawagar G5 za ta goyi bayan Tinubu idan ya nemi sake zabe a 2027.

4. Nyesom Wike

A watan Nuwamban 2023, Wike ya sha alwashin ba zai tsaya takara a zaben shugaban kasa na 2027 ba, domin ba zai kara da Shugaba Tinubu ba.

Da yake magana a wani shirin kai tsaye na gidan talbijin wanda Legit Hausa ta bibiya, Wike ya ce shi dan halas ne don haka ba zai yi takara a 2027 ba.

Kara karanta wannan

'Babban abu na shirin faruwa': Martanin yan Najeriya da Peter Obi ya ziyarci jigon APC a Kano

Kafin wannan lokacin, Wike, jigon jam’iyyar PDP, ya yi alkawarin tarawa Shugaba Tinubu kuri'u a zabe mai zuwa, inda ya ce jam'iyyun da suka samu kuri'u 2,000 a zaben 2023, ba za su samu komai a 2027 ba.

5. Ayodele Fayose

Fayose, wanda ya jagoranci jihar Ekiti a matsayin gwamna na PDP, ya tabbatar da cewa ya taka rawar gani a wajen faduwar jam'iyyar PDP a zaben 2023.

Rahoton Channels TV ya ce Fayose ya yi hamayya da Atiku Abubakar a zaben 25 ga Fabrairu, 2023 inda ya tarawa Tinubu ruwan kuri'u.

Sai dai idan har zai canza shawara a lokacin zaben 2027, ana kyautata zaton tsohon gwamnan jihar na Ekiti zai goyi bayan Tinubu da APC.

"Tinubu zai iya lashe zaben 2027" - Omokri

A wani labarin, mun ruwaito cewa Reno Omokri, tsohon hadimin shugaban kasa, ya yi magana kan yiyuwar Shugaba Bola Tinubu ya sake lashe zabe a 2027.

Kara karanta wannan

Abubuwan da 'yan Najeriya suka fada bayan Buhari ya yi kyautar daloli

Omokri ya yabawa Tinubu bisa iya juya tsofaffin abokan gaba zuwa abokai, tare da amfani da wannan dabarar wajen cimma burinsa na siyasa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.