Shugaban FIRS Zai Ajiye Kujerarsa domin Neman Gwamna? Gaskiya Ta Fito

Shugaban FIRS Zai Ajiye Kujerarsa domin Neman Gwamna? Gaskiya Ta Fito

  • Shugaban hukumar tattara kudin shiga ta FIRS, Zacch Adelabu Adedeji, ya yi magana kan jita-jitar tsaya wa takarar gwamna a jihar Oyo
  • Mr. Zacch ya ce burinsa shi ne mayar da hankali kan cika ayyukan da aka ɗora masa a yanzu ba tare da shiga siyasa ba
  • Adedeji ya nemi addu’a daga jama’a don samun nasarar kammala wa’adin aikin da ke gabansa ba tare da an karkatar masa da hankali ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Ibadan, Oyo - Shugaban Hukumar Tara Kudaden Shiga na Ƙasa (FIRS), Zacch Adelabu Adedeji ya mayar da martani kan rade-radin tsayawa takarar gwamna.

Adedeji ya bayyana cewa ba zai tsaya takarar kujerar gwamnan jihar Oyo a shekarar 2027 ba.

Shugaban FIRS ya yi magana kan neman takarar gwamna
Shugaban FIRS ya musanta shirin neman takarar gwamna a jihar Oyo. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Mr Zacch ya fadi burinsa a gwamnatin Tinubu

A cikin wata hira da ya yi kwanan nan a bainar jama’a, Adedeji ya ce zai mayar da hankali ne kan nauyin da aka daura masa, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Ajali ya yi: Sarki a Najeriya ya gamu mummunan hatsari, Allah ya yi masa rasuwa

Shugaban FIRS, wanda fitaccen ɗan siyasa ne da aka sani sosai a jihar, ya ce ya fi mayar da hankali kan cika ayyukansa na yanzu.

Tsohon kwamishinan kudi a Oyo ya ce babban burinsa shi ne sauke nauyin da Allah ya daura masa a hukumar FIRS.

Shugaban FIRS ya musanta tsayawa takarar gwamna

“Ina son amfani da wannan dama don amsa tambayoyin mutane da yawa, ni, Zacch Adedeji, ba zan tsaya takarar zaben gwamna a 2027 ba."
"Zuwa wannan lokaci, da yardar Allah, mun yi duk abin da Allah yake so mu yi a jihar, abin da kawai nake nema shi ne addu’o’in don samun damar ƙarasa abin da nake yi, ba na son wani abu ya karkatar da hankalina.”

- Zacch Adelabu Adedeji

Gwamna Makinde ya yi sababbin nade-nade

Kun ji cewa Gwamna Seyi Makinde ya yi wasu sababbin naɗe-naɗen da ba a taɓa yin irinsu ba a tarihin gwamnatin jihar Oyo.

Gwamnan na PDP, wanda a kwanakin baya aka yaɗa jita-jitar yana shirin neman takarar shugaban kasa a 2027, ya naɗa manyan sakatarori 45.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.