Yadda ‘Yan Siyasar Jihar Kano 4 Suka Zagaya Kujera 1 cikin Shekaru 8 a Gwamnatin Tarayya

Yadda ‘Yan Siyasar Jihar Kano 4 Suka Zagaya Kujera 1 cikin Shekaru 8 a Gwamnatin Tarayya

  • Muhammadu Buhari ya fara jawo Kawu Sumaila ya zama mai taimaka masa kan harkokin ‘yan majalisar wakilai
  • Tun daga wancan lokaci har zuwa yau, wannan kujera ta na ta yawo tsakanin ‘yan siyasar Kano ta tsakiya da ta Kudu
  • Hon. Umar Ibrahim El-Yakub da Hon. Nasiru Illa sun rike mukamin, sai Bashir Lado kuma ya samu makamancinsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Kamar an yi wa ‘yan siyasar Kano alkawarin kujerar mai ba shugaban kasa shawara a kan harkokin majalisar tarayya.

A cikin shekarun da ba su kai 10 ba, an samu mutane daga jihar Kano da shugaban kasa ya ba wannan babbar kujera a gwamnati.

Kano.
Bola Tinubu da Muhammadu Buhari sun tafi da mutanen Kano wajen raba mukamai Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Legit Hausa ta bibiyi yadda Muhammadu Buhari da Bola Tinubu suka rika dauko masu ba da shawara kan aikin majalisa daga Kano.

Kara karanta wannan

"Na cancanta," Sanatan APC ya bayyana shirinsa na neman zama shugaban ƙasa a 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan Kano da suka zama hadimai a harkar majalisa

1. Kawu Sumaila

Daily Trust ta tuna da Muhammadu Buhari ya nada Kawu Sumaila a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin majalisar (wakilai) a 2015.

Kafin nan ‘dan siyasar ya wakilci Takai da Sumaila a majalisar tarayya. Shekaru bayan barin kujerar ya zama Sanatan kudancin Kano.

2. Umar Ibrahim El-Yakub

Lokacin da Sumaila ya sauka daga kujerarsa, ya tafi neman takara a 2019, Premium Times ta ce an canza shi da Hon. Umar Ibrahim El-Yakub.

Umar Ibrahim El-Yakub ya na rike da kujerar mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara sai aka zabe shi cikin Ministoci a 2022.

3. Nasiru Illa

Har ila yau, daga jihar Kano dai aka maye gurbin Umar Ibrahim El-Yakub wanda Garba Shehu ya ce ya zama Ministan harkokin gidaje.

Kara karanta wannan

Gwamnati za ta dauki mataki bayan gano masu ɗaukar makamai, su aikawa miyagu

Sanarwar da aka fitar ta ce Nasiru Illa ya wakilci Tarauni a majalisar tarayya kuma kwararren akanta ne da ya yi karatu har a Ingila.

4. Basheer Lado

Shi kuma Bola Tinubu da ya zama shugaban kasa, ya zabi Basheer Lado ya zama mai ba shi shawara a kan sha’anin majalisa (ta dattawa).

Sanata Basheer Lado ya wakilci Kano ta tsakiya a PDP daga 2011 zuwa 2015. Rabiu Kwankwaso ya doke shi, daga baya sai ya dawo APC.

NNPP a rikicin siyasar Kano

Duk yadda Abba Kabir Yusuf yake da Rabiu Musa Kwankwaso, rahoto ya zo cewa ana so a shiga tsakaninsu a siyasa a 'yan kwanakin nan.

‘Yan kungiyar Abba tsaya da kafanka sun ce dole sai gwamnan Kano ya rabu da Madugun Kwankwasiyya idan ya na so ya yi aiki a ofis.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng