Albashi da Alawus: Sanatan APC Ya Bayyana Miliyoyin da Ake Tura Masa a duk Wata
- Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa, Orji Kalu, ya ce yana karbar Naira miliyan 14 duk wata a matsayinsa na dan majalisar dattawa
- Tsohon gwamnan jihar Abia ya ce Naira miliyan 14 da yake samu duk wata ba ya isarsa biyan bukatun mazabarsa da na ma’aikatansa
- Kalu ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da yake magana kan ce-ce-ku-cen da ake ci gaba da yi kan albashin ‘yan majalisar tarayya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Sanata Orji Uzor Kalu, mai wakiltar Abia ta Arewa, ya bayyana cewa ya na karbar Naira miliyan 14 duk wata a matsayinsa na dan majalisar tarayya.
Sanata Kalu ya kuma karyata ra’ayin cewa ‘yan majalisar dokokin Najeriya na rayuwa cikin walwala yayin da talakawa ke shan wahala.
Albashin da Sanata Kalu ke dauka
Ya bayyana hakan ne a zantawarsa da Channels TV, inda ya fayyace cewa wannan kudin ya shafi dukkanin kudaden da yake kashewa da ya hada da albashin ma’aikatansa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A yayin tattaunawar, sanatan ya ce:
“Ina samun Naira miliyan 14 a duk wata. Wannan kudin ya shafi komai na rayuwata da na mazabata da kuma na albashin masu yi mini hidima.
Sanata Kalu, wanda tsohon gwamnan jihar Abia ne, ya jaddada cewa da kyar Naira miliyan 14 ke wadatar da ayyukan da ya rataya a wuyansa, kamar tafiya mazabarsa da kula da ofishinsa.
Ce ce ku ce kan albashin sanatoci
Wannan bayani ya ba da haske game da gaskiyar kudaden da sanatoci ke samu a duk wata, wanda galibi ake boyewa kuma ake ci gaba da ce ce ku ce a kai.
Sanatan ya ce yin wannan jawabin da yake samu na da nufin inganta gaskiya da kuma kalubalantar ra'ayin jama'a game da albashin 'yan majalisa ke samu.
"Ina karbar N21m" - Sanata Sumaila
A wani labarin, mun ruwaito cewa Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP ya bayyana cewa yana karbar albashi da alawus alawus har Naira miliyan 21 duk wata.
Sanata Kawu Sumaila mai wakiltar Kano ta Kudu a majalisar dattawa ta 10, ya ce ‘yan majalisar tarayya ba sa sanya wa kansu albashi da alawus da ya wuce kima.
Asali: Legit.ng