2027: Kwankwaso Ya Magantu kan Zama Mataimakin Obi, Ya Fadi Sharudan da Za a bi

2027: Kwankwaso Ya Magantu kan Zama Mataimakin Obi, Ya Fadi Sharudan da Za a bi

  • Jagoran siyasar jihar Kano, Rabiu Kwankwaso ya magantu kan amincewa da tayin zama mataimakin Peter Obi
  • Kwankwaso ya fayyace ratan da ke tsakaninsa da Obi ta ɓangaren ilimi da kuma siyasa inda ya ce ya girme shi
  • Sai dai Kwankwaso ya ce a shirye ya ke domin yin magana da kowa kan lamarin amma bisa sharuda na gaskiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi magana kan zama mataimakin dan takarar shugaban kasa a LP, Peter Obi.

Kwankwaso ya ce ba shi da matsala da hakan amma shi ba sa'ansa ba ne a siyasa har ma da bangaren ilimi.

Kwankwaso ya mayar da martani kan zama mataimakin Peter Obi a 2027
Rabiu Kwankwaso ya bayyana ratan da ke tsakaninsa da Peter Obi a siyasa da ilimi. Hoto: @PeterObi.
Asali: Twitter

2027: Kwankwaso ya fadi ratansa da Obi

Kara karanta wannan

"Kar a karaya:" Goodluck Jonathan ya tura sakon karfafa gwiwa ga yan kasa

Jigon jam'iyyar NNPP ya bayyana haka ne a cikin wani bidiyo da @jrnaib2 ya wallafa a shafin X a yau Juma'a 4 ga watan Satumbar 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kwankwaso ya kawo misalai da suka shafi kokarin da ya yi a Kano da mukaman da ya rike inda ya kwatanta da na Peter Obi.

Sanatan ya ce shi yayan Obi ne siyasa kowa ya sani har ma da ilimi amma ya ce a shirye suke su yi magana da kowa.

"Ko da ake cewa na yi wa Peter Obi mataimaki, ma ce ni ba ni da matsala amma a kawo ka'idoji, mu ne yan Arewa aka raina cewa ba mu da ilimi, amma ni yayansa ne a siyasa, a ilimi ma PhD ne da ni."
"Ba mukamai daya muka rike ba, kokarinmu ma a mulki ba iri daya ba ne kowa ya sani a jiharsa da tawa."

Kara karanta wannan

'Babu abin da ya dame mu': Turji ya fito ya cika baki kan kisan Halilu Sububu

"Saboda haka muna jira mu yi magana da kowa amma duk abin da za a yi a yi shi cikin gaskiya."

- Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso

Martanin yan Obidients ga maganar Kwankwaso

Wasu daga cikin magoya bayan Obi sun yi fatali da maganar Kwankwaso inda suka ce ba su bukatarsa.

@MasterMaliq:

"Ba mu bukatarka, mun gode sosai."

@IamEkene:

"Har yanzu bai fahimci abin da ya faru da shi a 2023 ba, Obi ba sa'ansa ba ne a siyasa, kamata ya yi yana hada kansa da Datti, amma lokaci zai mayar da shi mai kan-kan da kai."

@Emegzyofficial:

"Kana ganin ka fi Peter Obi amma kana tashi da kuri'u miliyan biyu yayin da Obi ya samu miliyan shida, waye babba a cikinku."

@EzeigboChigozie:

"Kwankwaso ba abin yarda ba ne a bar shi kawai, yana taya Tinubu yaki ne, a karshe zai yaudari Peter Obi."

Kwankwaso ya koka kan yadda APC ke mulki

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Gwamna ya lissafo ni'imomi 3 a kasar nan, ya nemi a dage da addu'a

Kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya caccaki tsarin yadda jam'iyyar APC ke mulkin Najeriya a yanzu.

Kwankwaso ya koka kan yadda ake fama da tsadar rayuwa da kuma matsanancin rashin tsaro saboda sakaci na Bola Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.