Kwankwaso Ya Bayyana Abin da 'Yan Najeriya Za Su Yiwa APC a 2027

Kwankwaso Ya Bayyana Abin da 'Yan Najeriya Za Su Yiwa APC a 2027

  • Jagoran jam'iyyar NNPP na ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso, ya caccaki jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya
  • Kwankwaso ya bayyana cewa APC ta wahalar da ƴan Najeriya kuma za su sauya ta a zaɓen shekarar 2027 da ke tafe
  • Ya bayyana cewa a bayyana yake APC ba ta son talakawa kuma ƴan Najeriya za su yi fafutukar ganin sun kawar da ita daga kan madafun ikon ƙasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi magana kan halin ƙuncin da ake ciki a ƙasar nan.

Kwankwaso ya bayyana cewa duba da halin da ake ciki a ƙasar nan, ƴan Najeriya za su yunƙuro domin kawo sauyi a 2027.

Kara karanta wannan

Dan jam'iyyar PDP ya sauya sheka zuwa APC a zauren Majalisar tarayya

Kwankwaso ya caccaki APC
Kwankwaso ya ce 'yan Najeriya za su sauya APC a 2027 Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso
Asali: Facebook

Kwankwaso ya bayyana haka ne a lokacin da yake karɓar dimbin ƴaƴan jam’iyyar APC da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar NNPP a jihar, cewar rahotpn jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kwankwaso ya caccaki APC

Ya tarbi ƴan jam’iyyar APC da suka sauya sheƙar ne daga ƙananan hukumomin Dala, Kiru da Gwale a gidansa da ke Miller Road a Kano.

"Yan Najeriya musamman ƴan Arewa sun sha wahala sosai kuma babu wani matsin lamba ko tsoratarwa da zai sa su canja ra’ayinsu."
"Ya kamata ƴan Najeriya su sake tunani kan yadda abubuwa suke a halin yanzu, yanzu ta bayyana a fili cewa gwamnatin APC ba ta son talakawa kuma ba za ta taɓa canzawa ba."
"Yanzu ta tabbata cewa duk da shirinsu na amfani da jami’an tsaro da INEC a zaɓe mai zuwa, hakan ba zai yiwu ba saboda ƴan Najeriya sun gaji kuma tabbas za su yi fafutukar kawo sauyi."

Kara karanta wannan

Jam'iyyar PDP ta yi nasara kan APC ana shirin zaben gwamna

- Rabiu Musa Kwankwaso

Kwankwaso ya hango nasara a 2027

A wani labarin kuma, kun ji cewa jagoran jam'iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Rabi'u Kwankwaso, ya yi magana kan babban zaben Najeriya na 2027 da ke tafe.

Tsohon gwamnan jihar na Kano ya bayyana cewa jam'iyyar NNPP za ta taka rawar gani a zaben 2027 domin ta dauki manyan matakai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng