PDP da APC Sun Hada Kai domin Kalubalantar Matakin Gwamna kan Zabe

PDP da APC Sun Hada Kai domin Kalubalantar Matakin Gwamna kan Zabe

  • Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers na fuskantar matsala daga jam'iyyun PDP da kuma APC kan zaben ƙananan hukumomi
  • Jam'iyyun guda biyu sun kalubalanci gwamnan kan shirin gudanar da zaben a ranar 5 ga watan Oktoban 2024 duk da hukuncin kotu
  • Hakan ya biyo bayan fatali da umarnin kotu da gwamnan ya yi kan cigaba da shirin gudanar da zaben a ranar Asabar mai zuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Yayin da ake shirin gudanar da zabukan kananan hukumomi a jihar Rivers, APC da PDP sun hade baki.

Jam'iyyar APC mai adawa da PDP mai mulkin jihar sun kalubalanci shirin gudanar da zaben kananan hukumomin Ribas.

Kara karanta wannan

Nasarawa: NASIEC ta shirya gudanar da zaben ciyamomi, an fitar da jadawali

PDP da APC sun hade bakinsu domin kalubantar Gwamna Fubara
Jam'iyyun PDP da APC sun kalubalanci Gwamna Siminalayi Fubara kan zaben kananan hukumomi. Hoto: Sir Siminalayi Fubara.
Asali: Facebook

PDP da APC sun hada kai a Rivers

The Guardian ta ruwaito cewa jam'iyyun biyu na kalubalantar Gwama Siminalayi Fubara kan dogewa cewa sai an yi zabukan da aka shirya yi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan ya biyo bayan shirin gudanar da zaben a ranar Asabar 5 ga watan Oktoban 2024 duk da umarnin kotu a cewar rahoton Punch.

Shugaban riko na jam'iyyar APC a jihar, Cif Tony Okocha ya kalubalanci Fubara duba da hukuncin kotu kan dakatar da zaben da aka yi niyya.

A bangarensa, shugaban PDP a jihar, Chukwuemeka Aaron ya ce akwai kura-kurai a shirin gudanar da zaben inda ya ce jam'iyyarsu ba za ta shiga ba.

Gwamna Fubara ya sha alwashi kan zaben

Duk da barazanar jam'iyyun guda biyu, a jiya Laraba 2 ga watan Oktoban 2024 Gwamna Fubara ya ba da tabbacin gudanar da zaben

Kara karanta wannan

APC, PDP sun sha kashi: APGA ta lashe zaben duka ciyamomi a Kudancin Najeriya

Wannan umarni na gwamnan ya fara sanya fargaba a zukatan yan jihar saboda tsoron tashe-tashen hankula.

Gwamna Fubara ya ba da hukun zabe

Kun ji cewa Gwamnan jihar Ribas ya ayyana Alhamis da Jumu'a a matsayin ranakun hutu domin ba ma'aikata damar komawa yankunansu.

Siminalayi Fubara ya ce ya ɗauki wannan matakin ne domin mutane su koma gida su kaɗa kuri'unsu a zaɓen kananan hukumomi.

Ya kuma sanar da taƙaita zirga-zirgar ababen hawa daga tsakar daren ranar Juma'a zuwa ƙarfe 5:00 na yammacin ranar Asabar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.