Shugaban Kasa Tinubu Ya Tsawatarwa Yan Siyasa Ana Saura a yi Awanni Zaben Edo

Shugaban Kasa Tinubu Ya Tsawatarwa Yan Siyasa Ana Saura a yi Awanni Zaben Edo

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ja kunnen yan siyasa a jihar Edo kan gudanar da zabe cikin lumana
  • Shugaban ta sanarwar da hadiminsa,Bayo Onanuga ya fitar, ya ce ba a samun yalwar arziki sai da zaman lafiya
  • A ranar Asabar, 21 Satumba 2024 mazauna jihar Edo za su fita rumfunan zabe domin zabar sabon gwamna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Edo - Shugaban kasar nan, Bola Ahmed Tinubu ya bukaci masu ruwa da tsaki sun tabbatar an yi zaben Edo bisa adalci. Shugaban ya jaddada muhimmancin zaman lafiya yayin gudanar da zaben gwamnan jihar a Edo.

Kara karanta wannan

Ana gobe zaben Edo, Jonathan ya tura muhimmin sako ga INEC da jami'an tsaro

Tinubu
Shugaba Tinubu ya ja kunnen yan siyasa kan zaben Edo Hoto; Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

A sakon da hadimin shugaban, Bayo Onanuga ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa ana samun ci gaba ne kawai idan akwai zaman lafiya.

Bola Tinubu ya ja kunnen yan siyasar Edo

Jaridar This day ta wallafa cewa shugaban kasa, Bola Tinubu ya gargadi yan siyasa kan tayar da hankula yayin zaben Edo a gobe Asabar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya gargadi wakilan jam'iyyun siyasa da su guji tayar da tarzoma lokutan zaben, domin yan kasa su na da yancin zabar wanda zai wakilce su.

Edo: Shugaba Tinubu ya shawarci masu zabe

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya shawarci yan jihar Edo da za su zabi wanda su ke so a matsayin gwamna da su bi doka da oda wajen kada kur'arsu.

Tinubu ya jaddada cewa ba shi da shakku kan ingancin hukumar gudanar da zabe mai zaman kanta (INEC) da jami'an tsaro wajen gudanar da sahihin zabe.

Kara karanta wannan

Zaɓen gwamna 2024: Muhimman abubuwa 5 da ya kamata ku sani game da siyasar Edo

Ana shirin gudanar da zabe a Edo

A baya mun ruwaito cewa shirye-shirye sun yi nisa a jihar Edo, yayin da jami'an tsaro, hukumar gudanar da zabe mai zaman kanta ta kasa da yan siyasa ke kokarin ganin an yi zabe cikin nasara.

Baya ga jami'an gwamnati, kungiyoyin fararen hula sun bayyana fargabar cewa akwai kananan hukumomin da za a samu matsalolin tsaro, saboda yan siyasa sun ki sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.