Ministan Tinubu Ya Shiga Matsala bayan Ya Yiwa Wasu Gwamnoni Barazana

Ministan Tinubu Ya Shiga Matsala bayan Ya Yiwa Wasu Gwamnoni Barazana

  • Kungiyar NUF ta Arewa maso Gabas ta yi Allah wadai da abin da Ministan Abuja ya yi wanda ta kira da dabancin siyasa
  • Ƙungiyar ta ce barazanar da Wike ya yi wa gwamnonin PDP kwanan nan ta tona asirin munanan ɗabi'unsa da rashin ladabi
  • NUF ta yi ikirarin Wike ya fita hayyacinsa kuma ya kamata PDP da shugaban ƙasa Bola Tinubu su ɗauki mataki a kansa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Maiduguri, Borno - Ƙungiyar haɗin kan Arewa maso Gabas (NUF) ta buƙaci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya gaggauta tsige ministan Abuja, Nyesom Wike.

A cewar ƙungiyar bai kamata a ɗauki lamarin barazanar da Wike ya yiwa gwamnonin jam'iyyar PDP da wasa ba domin ba abin da za a lamunta ba ne.

Kara karanta wannan

TUC ta yi fatali da ƙarin farashin man fetur, ta aika sakon gaggawa ga Bola Tinubu

Bola Tinubu da Nyesom Wike.
NUF ta bukaci Shugaba Tinubu ya sauke ministan Abuja Nyesom Wike Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Nyesom Ezenwo Wike
Asali: Facebook

NUF ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, kamar yadda Tribune Nigeria ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wace barazana ministan Abuja ya yi?

Wannan dai na zuwa ne bayan ministan Abuja ya caccaki gwamnonin PDP waɗanda suka nuna goyon baya ga Gwamna Similanayi Fubara a rikicin siyasar Ribas.

Da yake jawabi bayan kaɗa kuri'a a zaben shugabannin PDP a Ribas, Wike ya yi barazanar kunno wa gwamnonin wuta a jihohinsu idan suka shiga rigimar.

Kalaman Wike dai sun ta da ƙura a fagen siyasar Najeriya, inda jam'iyyar PDP ta ce ba za ta bar lamarin ya wuce haka sakaka ba.

NUF ta bukaci Tinubu ya sauke Wike

Jaridar Blueprint ta tattaro cewa yayin da take martani kan lamarin, ƙungiyar NUF ta ce:

Kara karanta wannan

Nenadi Usman: An naɗa mace a matsayin shugabar jam'iyya ta ƙasa a Najeriya

"Kalaman Wike cewa duk gwamnan da ya tsoma baki a harkokin siyasar Ribas ba zai iya barci a jiharsa ba suna da haɗari.
"Wannan ya sa kungiyar NUF take rokon a gaggauta sauke Wike daga matsayin ministan babban birnin tarayya Abuja.
“Abin da ya aikata ya nuna bai cancanta ya rike wani mukami a gwamnati ba, ballantana ma wanda ya kai matsayin ministan babban birnin tarayya”.

Gwamnonin PDP sun yi martani

A wani rahoton kuma, gwamnonin jam'iyyar PDP sun yi martani kan kalaman da ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike ya yi.

Ƙungiyar gwamnonin a wata sanarwa ta bayyana kalaman tsohon gwamnan Rivers a matsayin waɗanda ba su dace ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262