“Hadama ba Za Ta Barsu ba”: Kwankwaso kan Hadakar Atiku da ’Yan Adawa a 2027

“Hadama ba Za Ta Barsu ba”: Kwankwaso kan Hadakar Atiku da ’Yan Adawa a 2027

  • Tsohon kwamishina a jihar Kano, Musa Ilyasu Kwankwaso ya yi magana kan hadakar jiga-jigan jam'iyyun adawa game da zaben 2027
  • Kwankwaso ya ce Atiku Abubakar da Rabiu Kwankwaso da Peter Obi suna bata lokacinsu ne kan shirin kifar da Bola Tinubu
  • Wannan na zuwa ne yayin da jiga-jigan jam'iyyun adawa suke shirin haɗaka ta musamman domin shirin zaben 2027 mai zuwa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Jigon jam'iyyar APC a jihar Kano ya yi magana kan hadakar Atiku Abubakar da Peter Obi da Rabiu Kwankwaso.

Musa Ilyasu Kwankwaso ya ce duka bata lokacinsu suke yi wurin hadaka saboda zaben 2027 mai zuwa.

Kara karanta wannan

Ganduje: Tinubu, Buhari da wasu ƙusoshin APC za su yanke makomar shugaban APC

Kwankwaso ya caccaki Atiku da yan jam'iyyun adawa kan zaben 2027
Musa Ilyasu Kwankwaso ya magantu kan hadakar Atiku da ’yan adawa kan zaben 2027. Hoto: Rabi'u Musa Kwankwaso, Atiku Abubakar.
Asali: Facebook

2027: Kwankwaso ya magantu kan jam'iyyun adawa

Kwankwaso ya bayyana haka ne ga yan jaridu a yau Talata 3 ga watan Satumbar 2024, cewar rahoton Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigon na APC ya ce babu inda tafiyar za ta je duba da yadda suka yi a baya da kuma hadamar kowa a cikinsu.

Ya ce tarihi zai maimaita kansa ne saboda a baya sun hadu amma da yake kowa yana da haɗama da buri tafiyar ba ta je ko ina ba.

"An yi irin wannan haɗaka amma ta tarwatse saboda kowa yana da burukansa da mugun haɗama."
"A cikinsu babu wanda zai iya janyewa wani saboda yawan buri da kuma son kai da suke da shi."

- Musa Ilyasu Kwankwaso

Kwankwaso ya bugi kirji kan nasarar Tinubu

Kwankwaso ya ce yana da tabbacin Bola Tinubu zai samu nasara a karo na biyu saboda ayyukan alheri da ake yi.

Kara karanta wannan

2027: Shekarau zai jagoranci tawaga mai karfi domin kifar da Tinubu, sun fara shiri

Jigon APC ya ce tabbas haka zai zama cikin sauki saboda samun goyon baya da al'umma ke ba jam'iyyar.

Kwankwaso ya fadi mai daukar nauyin zanga-zanga

Kun ji cewa jigon jam’iyyar APC a jihar Kano, Musa Ilyasu Kwankwaso ya yi magana kan rikicin da aka samu a jihar sakamakon zanga-zanga.

Iliyasu Kwankwaso ya yi kira ga Bola Tinubu da ya ɗorawa Gwamna Abba Kabir Yusuf alhaki kan ɓarna da asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya yabawa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso bisa gargadi da kuma kira da ya yi na kada mutane su fito kan tituna domin yin zanga-zanga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.