Cikakken Jerin Jihohin da Za a Gudanar da Zabe a Watan Satumba

Cikakken Jerin Jihohin da Za a Gudanar da Zabe a Watan Satumba

  • Jihohin Edo, Kwara da Anambra su ne jihohi uku da za a gudanar da zaɓe a Najeriya a cikin watan Satumban 2024
  • A jihar Edo al’ummar jihar za su fito kaɗa ƙuri’a domin zaɓen sabon gwamna tsakanin jam’iyyar PDP mai mulki da jam’iyyun adawa na APC da Labour Party
  • Za kuma a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a jihar Anambra dake yankin Kudu maso Gabas da kuma jihar Kwara dake yankin Arewa ta Tsakiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Aƙalla jihohi uku ne za su gudanar da zaɓuɓɓuka a Najeriya a cikin watan Satumban 2024.

Zaɓuɓɓukan dake tafe sun haɗa da na ƙananan hukumomi zuwa zaɓen gwamna a jihar Edo.

Jihohin da za a yi zabe a Satumba
Mutanen jihar Edo za su zabi sabon gwamna a watan Satumba Hoto: @NGFSecretariat, @GovernorObaseki, @CCSoludo
Asali: Twitter

Gwamnonin jihohi da dama sun fara gudanar da zaɓuɓɓukan ƙananan hukumomi biyo bayan hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke kan cin gashin kan ƙananan hukumomi.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya shiga ganawa da shugaban China, an samu bayanai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jihohin da za a yi zaɓe a watan Satumba

Ga jerin jihohin da za a yi zaɓe a watan Satumba na 2024:

Zaɓen gwamnan jihar Edo

Al'ummar jihar Edo za su fito domin zaɓen sabon gwamna a ranar, 21 ga watan Satumban 2024, kamar yadda hukumar zaɓe ta INEC ta tsara.

Ƴan takarar da ke kan gaba a zaɓen sun haɗa da Asue Ighodalo na jam’iyyar PDP, Sanata Monday Okpebolo na jam’iyyar APC da Olumide Akpata na jam’iyyar Labour Party.

Hakazalika, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta bayyana cewa an karɓi katunan zaɓe 125,928 daga cikin sababbin katunan zaɓe na dindindin 184,438 a jihar Edo.

Zaɓen ƙananan hukumomi a Anambra

Gwamnatin jihar Anambra ƙarƙashin jagorancin Gwamna Charles Chukwuma Soludo, ta shirya gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a ranar Asabar, 28 ga watan Satumban 2024.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun jefa bama bamai a hedkwatar ƴan sanda, sun tafka ta'asa

Zaɓen na zuwa ne shekara 10 bayan an yi zaɓen ƙananan hukumomi a jihar wacce ke a yankin Kudu maso Gabas na Najeriya.

Shugabar hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Anambra (ANSIEC), Genevieve Osakwe, ta bayyana cewa ana shirye-shiryen gudanar da zaɓen ba tare da wata tangarɗa ba.

Zaɓen ƙananan hukumomi a Kwara

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kwara (KWSIEC) ta bayyana cewa za ta gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a jihar a ranar 21 ga watan Satumba, cewar rahoton jaridar The Punch.

A cewar sanarwar da hukumar ta fitar, ana ƙoƙarin ganin an gudanar da zaɓen a ranar da aka tsara.

Jam'iyyar APC ta lashe zaɓe a Kebbi

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam’iyyar APC ta lashe dukkanin kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 21 da Kansiloli 225 a jihar Kebbi.

A ranar Asabar, 31 ga watan Agustan 2024 hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kebbi (KESIEC) ta gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a faɗin jihar.

Kara karanta wannan

Tofa: Ƴan sanda sun bayyana Bature da ya nemi kifar da gwamnatin Tinubu a Najeriya

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar ta lashe dukkanin kujeru a zaɓen wanda aka fafata tsakanin jam'iyyun siyasa 17.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng