Bakin Jinin APC Zai Shafe Ku ": Dan Takarar NNPP Ya Soki Masu Komawa Jam'iyyar

Bakin Jinin APC Zai Shafe Ku ": Dan Takarar NNPP Ya Soki Masu Komawa Jam'iyyar

  • Dan takarar gwamna a zaben jihar Ondo a jam'iyyar NNPP, Olugbenga Edema ya caccaki wadanda suka koma APC
  • Edema ya ce ya tabbata sun jahilci yadda APC ta ke a Ondo da kuma kiyayya da yan jihar ke nuna mata a fili
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake shirin gudanar da zaben jihar a ranar 16 ga watan Nuwambar 2024 da muke ciki

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ondo - Dan takarar gwamna a jihar Ondo karkashin jam'iyyar NNPP, Olugbenga Edema ya yi magana kan wadanda suka koma APC.

Edema ya caccaki wadanda suka sauya sheka zuwa APC inda ya ce sun tafka babban kuskure a siyasa.

Kara karanta wannan

NEC: Ana rade radin kwace kujerar Ganduje, APC ta tsaida ranar taron da ake jira

Dan takarar NNPP a zaben gwamnan Ondo ya soki yan APC
Dan takarar NNPP a zaben gwamnan Ondo, Olugbenga Edema ya soki masu komawa APC. Hoto: Legit.
Asali: Original

Dan takarar NNPP a Ondo ya soki APC

'Dan takarar ya ce haka ya nuna cewa ba su san yadda jam'iyyar APC take ba a jihar Ondo, cewar The Guardian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Edema ya ce da sun sani kuwa da ba su shiga APC ba saboda jam'iyyar ba ta da dan takarar gwamna a zaben watan Nuwambar 2024.

Har ila yau, ya ce tsarin da aka bi wurin samar da Gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin zaɓaɓɓen dan takara ya saba ka'ida.

Ondo: Edema ya shawarci masu shiga APC

"Ya kamata su fahimci yadda al'umma suka ki jinin APC da kuma yadda aka yi zanga-zangar adawa da mulkin APC."
"Ubangiji da kansa ba ya tare da gwamnatin Aiyedatiwa saboda shi ba ya goyon bayan gurbatacciyar gwamnati."

- Olugbenga Edema

Wannan na zuwa ne yayin da ake shirin gudanar da zaben jihar a ranar 16 ga watan Nuwambar 2024 na wannan shekara.

Kara karanta wannan

Rikici ya ɓarke a APC bayan ta rabu gida 2 a jihar Arewa, gwamna ya yi gargadi

Mukarraban Mimiko sun sauya sheka zuwa APC

Kun ji cewa jam'iyyar PDP reshen jihar Ondo ta gamu da gagarumin koma baya yayin da ake shirye-shiryen zaɓen gwamna a wannnan shekarar.

Abokan siyasa da makusantan tsohon gwamnan jihar, Olusegun Mimiko, da manyan jiga-jigai sauya sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APC.

Waɗanda suka sauya shekar sun haɗa da tsohon ɗan majalisar tarayya, Hon Victor Akinjo da tsohon kakakin majalisar dokokin Ondo, Hon Joseph Akinlaja.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.