Duk da Rigima Kan Sahihancinsa a Jam’iyyar, APC Ta Ba Yaron Wike Mukami

Duk da Rigima Kan Sahihancinsa a Jam’iyyar, APC Ta Ba Yaron Wike Mukami

  • Ministan Abuja, Nyesom Wike na cigaba da mamayar APC yayin da aka nada na hannun damansa mukami a jam'iyyar
  • Jam'iyyar ta nada Ojukaye Flag-Amachree daga cikin mambobin kwamitin zaben jihar Edo da ake shirin yi a watan Satumba
  • Wannan nadin na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gudanarwa na jam'iyyar, Sulaiman Muhammad Argungu ya fitar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Jam'iyyar APC ta ba na hannun daman Ministan Abuja, Nyesom Wike mukami a kwamitin kamfe na zabe.

Jam'iyyar ta nada Ojukaye Flag-Amachree a matsayin mamban kwamitin kamfe na zaben jihar Edo da ke tafe.

Yaron Wike ya samu mukami a jam'iyyar APC
Jam'iyyar APC ta nada yaron Nyesom Wike mukami a kwamitin kamfe na zaben jihar Edo. Hoto: Nyesom Wike, Ojukaye Flag-Amachree.
Asali: Facebook

Jam'iyyar APC ta nada yaron Wike mukami

Kara karanta wannan

Gwamnoni sun shiga taro a Abuja ana shirin zanga zanga, an gano abubuwa 3

Sakataren gudanarwa na jam'iyyar, Sulaiman Muhammad Argungu shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar, cewar Daily Nigerian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Argungu ya yaba da irin jajircewar Flag-Amachree ga jam'iyyar duba da irin gwagwarmayar da ya yi wurin cigaban jam'iyyar.

Wannan nadin na zuwa ne yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben gwamnan jihar a watan Satumbar 2024, Pulse ta tattaro.

APC ta shawarci Flag-Amachree kan aiki tukuru

"Wannan nadin naka a kwamitin zaben ya biyo bayan jajircewa da kake da shi da kuma nuna kwarewa a siyasa na tsawon shekaru."
"A matsayin mamban kwamitin zaben jihar Edo, ana bukatar ka yi amfani da duka kwarewarka a siyasa da sauran lamura domin tabbatar da nasarar dan takararmu a zabe."

- Sulaiman Muhammad Argungu

Wannan nadin na zuwa ne kasa mako daya bayan shugaban jam'iyyar APC, Abdullahi Ganduje ya kafa kwamitin kamfen a ranar 20 ga watan Yulin 2024.

Kara karanta wannan

Ana zargin an rabawa 'yan majalisa cin hancin N400m domin amincewa da bukatar Tinubu

Wike ya caccaki masu daukar nauyin zanga-zanga

Kun ji cewa Ministan Abuja, Nyesom Wike a ranar Talata, 23 ga watan Yulin 2024 ya nuna rashin jin dadinsa game da shirin gudanar da zanga-zanga.

Wike ya bayyana zanga-zangar da aka shirya yi a watan Agustan shekarar 2024 a matsayin wacce za a yi saboda siyasa domin biyan buƙatar wasu tsiraru.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.