Tsohon Kwamishina Ya Fallasa Gwamnati, An Gano Uba Sani Yana ‘Karya’ da Ayyukan El Rufai

Tsohon Kwamishina Ya Fallasa Gwamnati, An Gano Uba Sani Yana ‘Karya’ da Ayyukan El Rufai

  • Jafaru Sani ya fito ya kare Nasir El-Rufai wanda ‘yan majalisar dokokin jihar Kaduna suka taso shi a gaba
  • Tsohon kwamishinan ya musanya zargin da ake yi a kan batun bashi, ya yi bayanin irin ayyukan da aka yi
  • ‘Dan siyasar ya zargi Uba Sani da fakewa da ayyukan da aka yi tun a gwamnatin El-Rufai, yana nuna nasu ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Kaduna - Jafaru Sani ya dauki lokaci ya kare gwamnatin Nasir El-Rufai daga zargin cewa ta yi awon gaba da dukiyar al’ummar Kaduna.

Akwai zargin da majalisar dokoki ta ke yi na cewa an karkatar da N423bn a lokacin da Nasir El-Rufai ya yi mulki daga 2015 zuwa 2023.

Kara karanta wannan

Samoa: Bashir Aliyu Umar ya fadi matakin da majalisar shari’a za ta dauka kan gwamnati

Uba Sani da El-Rufai
An zargi Uba Sani da neman suna da ayyukan Nasir El-Rufai a Kaduna Hoto: @BashirElRufai/@IU_Wakilii
Asali: Twitter

Kwamishinan Nasir El-Rufai ya kare shi

A wani fai fai da wani Imran U Wakili Oluwa Femi ya wallafa a shafin X, Jafaru Sani ya musanya wadannan zargi, har ya yi martani.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton kwamitin binciken majalisar Kaduna ba komai ba ne face karya da soki-burutsu a wajen Jafaru Sani wanda ya yi kwamishina.

El-Rufai da zargin 'yan majalisar Kaduna

Amma a wata hira da aka yi wani ‘dan majalisar dokokin Kaduna a tashar Channels, ya bayyana akasin ikirarin Malam Ja’afar Sani.

Honarabul Henry Marah ya ce majalisa ba ta amince da wasu daga cikin bashin da gwamnatin Malam Nasir El-Rufai ta karbo ba.

Tsohon kwamishinan ya ce suna nan a kan bayanin da El-Rufai ya yi game da basussukan jihar a lokacin da yake mika mulki.

Uba Sani yana dauraye ayyukan El-Rufai?

Kara karanta wannan

Alkali ya yi barazanar daure Hadimin Gwamna Abba kan shari'ar Ganduje

Har ila yau, Jafaru Sani ya caccaki gwamnatin Uba Sani da ya zarga da ikirarin ita ta yi wasu ayyuka da a zamanin El-Rufai aka yi su.

An yi misalai da katafaren dakin bincike, makarantun kimiyya da wasu 62 a karkashin tsarin Agile da kayan asibitocin shan magani 250.

Sannan ya yi karin haske cewa cikin ayyukan da Uba Sani yake tunkaho da su akwai wadanda tun kafin El-Rufai aka samo kudinsu.

Malam Jafaru Sani yana maida martani ne ganin gwamnatin Kaduna ta na kukan an ci bashi kuma ba a san ina kudin suka shige ba.

Gwamna Uba ya koka da bashin El-Rufai

Kwanaki aka samu labari Gwamna Uba Sani ya fadi bashin da aka ci a Kaduna da kudin da Nasir El-Rufai ya bari a asusun jihar Kaduna.

Uba Sani ya ce kason jihar na tafiya ne a biyan bashin da aka ci. Sai dai shi ya dafe aka karbo bashin a lokacin yana majalisar dattawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng