Sarautar Kano: An Zargi Kwankwaso da Rubutawa ’Yan NNPP a Majalisa Wasika Kan Tinubu

Sarautar Kano: An Zargi Kwankwaso da Rubutawa ’Yan NNPP a Majalisa Wasika Kan Tinubu

  • Kungiyar Progressive League of Youth Voters ta zargi Sanata Rabiu Musa Kwankwaso kan yadda za a caccaki Bola Tinubu
  • Kungiyar na zargin Kwankwaso da rubuta wasika ga 'yan Majalisa na NNPP kan korafi kan tsoma bakin Bola Tinubu a rigimar sarauta
  • Jagoran kungiyar na kasa, Ambasada Abdul Usman Shaibu shi ya yi wannan zargi a jiya Litinin 1 ga watan Yulin 2024 a Abuja

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Wata kungiya ta zargi Sanata Rabiu Kwankwaso da neman hada kan 'yan Majalisar Tarayya na NNPP domin caccakar Bola Tinubu.

Kungiyar mai suna Progressive League of Youth Voters ta ce Kwankwaso ya dauki matakin ne kan zargin hannun Tinubu a rigimar masarautar jihar.

Kara karanta wannan

"Suna neman kassara Tinubu", Kungiyar Arewa ta caccaki Atiku da El Rufai kan ziyartar Buhari

An zargi Kwankwaso da neman hadin kan 'yan Majalisar NNPP kan rigimar sarautar Kano
Kungiyar matasa ta zargi Kwankwaso da rubuta wasika ga 'yan Majalisar NNPP kan Bola Tinubu. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Sarautar Kano: Kungiya ta zargi Rabiu Kwankwaso

Shugaban kungiyar a Najeriya, Ambasada Abdul Usman Shaibu ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da Legit ta samu a jiya Litinin 1 ga watan Yulin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kungiyar ta zargi Kwankwaso ya rubuta takarda ga duka 'yan Majalisun NNPP domin kaddamar da shirin da zarar an dawo zaman Majalisar.

Shaibu ya ce Kwankwaso na zargin Tinubu da hannu dumu-dumu a rigimar masarautun jihar Kano ya ake ci ki a yanzu.

Ya ce an rubuta takardar a ranar 24 ga watan Yunin 2024 ga 'yan Majalisar NNPP a Tarayya da kuma na jihohi a cewar Pulse.

An zargi Kwankwaso da neman caccakar Tinubu

Kwadinetan ya ce Kwankwaso a cikin takardar ya bukaci mambobin su fara korafin a zaman Majalisar a Abuja kan zargin Tinubu da hannu a rigimar.

Kara karanta wannan

"Kamar kowa kake a yanzu": Abba Kabir ya fayyace matsayin Aminu Ado a Kano

"Muna da tabbaci kan wasikar da Kwankwaso ya rubuta ga duka mambobin NNPP a Majalisar Tarayya."
"A cikin wasikar, Kwankwaso ya bukaci su yi amfani da ikonsu wurin matsawa Bola Tinubu da Gwamnatin Tarayya kan cire hannu a rigimar masarautun Kano."
"Ya kuma bukaci 'yan Majalisar su goyi bayan gwamnatin jihar Kano da Gwamna Abba Kabir Yusuf."

- Abdul Usman Shaibu

Kwankwaso ya maka EFCC a kotu

Kun ji cewa Babbar kotun jihar Kano za ta fara zaman sauraron ƙorafin da Rabiu Kwankwaso da wasu mutum bakwai suka shigar da EFCC.

Jagoran NNPP da sauran mutanen su bakwai sun maka hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC a gaban kotun ne kan abin da ya shafi tauye haƙƙinsu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel