"Ka Gyara Kalamanka, Kai Ba Jinin Sarauta Ba Ne": Basarake Ya Kunyata Ɗan Takarar Gwamna

"Ka Gyara Kalamanka, Kai Ba Jinin Sarauta Ba Ne": Basarake Ya Kunyata Ɗan Takarar Gwamna

  • Ɗan takarar gwamna ya ji wani iri bayan basarake ya ba shi kunya a gaban jama'a kan ikirarin kasancewa jinin sarauta
  • Oba na Benin, Mai Martaba Ewuare II ya ci gyaran ɗan takarar gwamnan jihar Edo a jami'yyar LP, Olumide Akpata kan kalamansa
  • Hakan ya biyo bayan ziyarar ɗan takarar fadar basaraken inda ya ce shi jinin sarauta ne a fadar da ke masarautar Benin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Edo - Mai Martaba, Oba na Benin, Oba Ewuare II ya ci gyara ɗan takarar gwamnan jihar Edo, Olumide Akpata.

Basaraken ya ci gyaran ɗan takarar ne a jam'iyyar LP bayan ya bayyana kansa a matsayin jinin sarauta.

Kara karanta wannan

Sanusi II ya yi hawa: 'Yan sanda sun yi magana kan yadda aka yi Sallar Idi a Kano

Basarake ya kunyata ɗan takarar gwamna a Edo
Oba na Benin, ya ci gyaran ɗan takarar gwamna a Edo, Olumide Akpata kan cewa shi jinin sarauta ne. Hoto: @Naija_PR/@thecableng.
Asali: Twitter

Edo: Basarake ya ci gyaran ɗan takara

Wannan na zuwa ne bayan Akpata da Peter Obi sun ziyarci basaraken a fadarsa a faifan bidiyo da Vanguard ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin ziyarar Akpata ya bayyana kansa a matsayin jinin sarauta cikin yarensa na asali da kuma turanci.

Daga bisani basaraken a cikin faifan bidiyon ya yi fatali da maganar inda ya ce Akpata ba shi da alaka da sarauta ko ta wace hanya.

"Kai jajirtaccen dan kasa ne mai kokari, amma maganar kana da alaka da masarautar nan akwai kuskure."
"Duk ƴaƴana babu mai neman takara ko wanda ya tsunduma harkar siyasa, ina son fayyace hakan ga al'umma da kuma kafofin yada labarai."

- Oba Ewuare II

Edo: Martanin Akpata ga basaraken

Yayin da yake martani, Akpata ya ce tabbas ba zai iya zama jinin sarauta ba amma kuma shi ɗan masarautar ne.

Kara karanta wannan

Babbar Sallah: An bayyana jihar da Shugaba Tinubu zai yanka ragon layyarsa

Miyagu sun farmaki dan takara a Edo

A wani labarin, kun ji cewa wasu bata gari sun farmaki dan takarar gwamnan jihar Edo karkashin jam'iyyar LP, Olumide Akpata.

Akpata ya zargi babban jami'in gwamnatin jihar da daukar nauyin harin da aka kai masa a Jami'ar Benin.

Lamarin ya faru ne a ranar Juma'a 12 ga watan Afrilu a cikin Jami'ar yayin wani babban taro da aka gudanar ana daf da zaben jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel