Jigon APC, Salihu Lukman Ya Nakasa Jamiyyar Bayan Ya Yi Murabus, Ya Jero Dalillai

Jigon APC, Salihu Lukman Ya Nakasa Jamiyyar Bayan Ya Yi Murabus, Ya Jero Dalillai

  • Jam'iyyar APC ta yi babban rashi bayan jigonta ya watsar da ita saboda rashin tsare-tsare masu amfani ga ƴan ƙasa
  • Tsohon mataimakin shugaban APC a Arewa maso yamma, Salihu Lukman ya bayyana haka ne a yau Laraba 12 ga watan Yuni
  • Lukman ya dade yana caccakar Gwamnatin Bola Tinubu da jam'iyya mai mulki ta APC kan rashin iya shugabanci

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC a Arewa maso Yamma, Salihu Lukman ya yi murabus.

Lukman ya zargi jamiyyar da rashin iya shugabanci da kuma munanan tsare-tsare wanda ya jefa kasar a halin kunci.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta fadi ranar da shugaba Tinubu zai yiwa 'yan Najeriya jawabi

Jigon jami'yyar APC, Lukman ya yi murabus
Salihu Lukman ya watsar da jam'iyyu APC bayan ya yi murabus. Hoto: @PO_GrassRootM.
Asali: Twitter

Jigon APC ya yi murabus daga jam'iyyar

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu a yau Laraba 12 ga watan Yuni a Abuja, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tsohon darakta-janar na kungiyar gwamnonin bai fadi matakin da zai dauka na gaba ko jam'iyyar da zai koma ba.

Sai dai Lukman ya ce ya hada kai da wasu manyan shugabannin siyasa domin tunkarar zaben 2027, cewar TheCable.

"Duk da haka, mutum zai iya kasancewa a jam'iyyar APC idan Tinubu zai kawo gyara a tsare-tsare kamar yadda ainihin tsarinta ya ke."
"Batun gaskiya a yanzu kasancewa ta a jam'iyyar ba shi da amfani kuma babu bukatar na ci gaba da cusa kaina a cikinta."
"Za mu yi zama da jajirtattun ƴan Najeriya wandanda suka amince wurin bunkasa dimukradiyya da ci gabanta a Najeriya."

Kara karanta wannan

"An maida rai ba komai ba," Atiku ya riga shugaban kasa ta'aziyyar kisan Katsina

- Salihu Lukman

APC: Lukman ya bayyana shirinsa na gaba

Jigon APC da ke Kaduna ya ce yana da tabbacin nan gaba za a samar da shugabanni da za a kawo sauyi a rayuwar ƴan Najeriya.

Ya ce ba ya tsammanin shugabannin jam'iyyar za su aminta da hukuncin da ya yanke amma daga bisani za a hada kai domin inganta dimukradiyya a Najeriya tare gaba daya.

Jigon APC ya yi murabus a Edo

Kun ji cewa APC a jihar Edo ta samu koma baya bayan babban jigo a jam'iyyar ya yi murabus yayin da ake tunkarar zaɓen gwamnan jihar.

Cif Francis Inegbeneki mataimakin shugaban jam'iyyar na mazaɓar Sanatan Edo ta Tsakiya, ya yi murabus daga jam'iyyar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel