"Kanku Ake Ji": El Rufai Ya Bugi Kirji, Ya Yi Zazzafan Martani Kan Zargin Badaƙala a Kaduna

"Kanku Ake Ji": El Rufai Ya Bugi Kirji, Ya Yi Zazzafan Martani Kan Zargin Badaƙala a Kaduna

  • Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya magantu kan binciken da kwamitin Majalisar jihar ta gudanar game da gwamnatinsa
  • El-Rufai ya ce wannan mataki na kwamitin Majalisar kawai bita da kullin siyasa ne amma ya gudanar da gwamnatinsa cikin gaskiya
  • Hakan na zuwa ne bayan kwamitin ya bukaci hukumar yaki da cin hanci ta cafke El-Rufai kan zargin badakala a lokacin mulkinsa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya yi martani kan zargin badakala a gwamnatinsa.

El-Rufai ya yi fatali da rahoton Majalisar dokokin jihar kan binciken gwamnatinsa daga shekarar 2015 zuwa 2023.

El-Rufai ya magantu kan binciken gwamnatinsa da ake yi a Kaduna
Nasiru El-Rufai ya caccaki binciken gwamnatinsa a Kaduna, ya ce bita da kullin siyasa ne. Hoto: Nasir El-Rufai.
Asali: Twitter

Kaduna: El-Rufai ya magantu kan zargin gwamnatinsa

Kara karanta wannan

Tsohon gwamnan CBN ya shiga tasku, kotu ta ƙwace manyan kadarorinsa na N11.1bn

Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne ta bakin kakakinsa, Muyiwa Adekeye a yau Laraba 5 ga watan Yuni, cewar Channels TV.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce wannan matakin Majalisar kawai bita da kullin siyasa ne inda ya tabbatar da cewa ya jagoranci gwamnati mai tsafta yayin mulkinsa, Punch ta tattaro.

"Nasir El-Rufai yana alfahari da ayyukan alheri da ya gudanar a jihar Kaduna yayin da ya ke gwamna."
"Mafi yawan wadanda suka yi gwamnati da El-Rufai sun gurfana a gaban kwamitin wanda ke nuna kwarin guiwa kan irin gwamnatin da ya gudanar."
"El-Rufai yana ba ƴan Najeriya tabbacin cewa ya gudanar da mulki cikin gaskiya da bin doka tare da taimakon mukarrabansa kwararru."
"Ya bukaci a yi fatali da wannan bincike na son rai da kuma bita da kullin siyasa da ake yi."

- Muyiwa Adekeye

Majalisar Kaduna ta bukaci gurfanar da El-Rufai

Kara karanta wannan

Mafi karancin albashi: Akwai yiwuwar kungiyar NLC ta amshi tayin gwamnati

Wannan na zuwa ne bayan kwamitin Majalisar ya bukaci a hukunta El-Rufai da mukarrabansa saboda zargin badakala a gwamnatinsa.

Har ila yau, kwamitin ya bukaci dakatar da kwamishinan kudi a Kaduna, Shizer Badda wanda ya rike mukami a gwamnatin Nasir El-Rufai.

Bello El-Rufai ya magantu kan Uba Sani

Kun ji cewa 'dan Majalisar Tarayya a jihar Kaduna, Bello El-Rufai ya yi martani kan alakarsa da mai girma Gwamna Uba Sani.

Hon. Bello El-Rufai ya ce har yanzu Mai girma Gwamna Uba Sani mai gidansa ne kuma ya dauke shi abin koyi a rayuwarsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel