"Sun Lalata Komai": Tsohon Shugaban Kasa Ya Koka Yadda Aka Ruguza Ayyukansa

"Sun Lalata Komai": Tsohon Shugaban Kasa Ya Koka Yadda Aka Ruguza Ayyukansa

  • Tsohon shugaban kasar Najeriya, Dakta Goodluck Jonathan ya koka kan yadda aka lalata tsare-tsaren da ya kawo
  • Jonathan ya ce a lokacin mulkinsa ya yi kokarin kawo ayyukan ci gaba amma bayan tafiyarsa sai da aka lalata komai
  • Legit Hausa ta tattauna da wani jigon jam'iyyar PDP a Gombe kan wannan martani na Goodluck Jonathan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya bayyana yadda ya kawo abubuwan ci gaba a Najeriya.

Jonathan ya ce ya kawo tsare-tsare da zasu inganta kasar amma bayan barin mulki an lalata komai.

Tsohon shugaban kasa ya fadi yadda aka lalata ayyukan alheri da ya kawo Najeriya
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya magantu kan ayyukan alheri da ya kawo Najeriya. Hoto: Pius Utomi Ekpei.
Asali: Getty Images

Ayyukan alheri da Jonathan ya kawo Najeriya

Tsohon shugaban kasar ya bayyana haka ne a bikin cika shekaru 25 na Jami'ar Igbinedion da ke jihar Edo a yau Juma'a 10 ga watan Mayu, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

Ba a gama da matsalar gida ba, Tinubu ya yi alkawari ga shugaban Chadi, Deby

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Goodluck ya ce ya tabbatar da ba mata guraben karatu a makarantar NDA da ke Kaduna amma ya fuskanci kalubale kan kudirin nasa.

Sai dai ya ce a matsayinsa na shugaban kasa sai da ya nemo hanyar tabbatar da ganin ya aiwatar da abin da ya yi niyya, Punch ta tattaro.

Jonathan ya bukaci a ba mata dama

Jonathan ya bukaci a ba mata dama domin tabbatar da ci gabansu a dukkan bangarorin kasar ba tare da nuna wariya ba.

"Na tuno kalubalen da mata ke fuskanta a aikin soja, a matsayina na shugaban kasa na umarci ba mata guraben karatu a makarantar NDA."
"Duk wasu ayyuka da dama da na kawo na ci gaba musamman a bangaren fasaha an lalata su."

- Goodluck Jonathan

Legit Hausa ta tattauna da jigon PDP

Legit Hausa ta tattauna da wani jigon jam'iyyar PDP a Gombe kan wannan martani na Goodluck Jonathan.

Kara karanta wannan

Tinubu ya tausaya, ya dakakar da tsarin biyan harajin 0.5% da CBN ya kawo

Aliyu Abdulkadir ya ce abin da ya fadi gaskiya ne ganin yadda PDP suka yi mulkin adalci.

Aliyu ya ce ko a mukin marigayi tsohon shugaban kasa Yar'adua kowa ya san yadda aka yi mulki duk da karantan lokaci da ya samu.

"Babu tantama mulkin shugabannin PDP daban ya ke da irin salon mukin jam'iyyar APC tun daga 1999 zuwa yanzu."

- Aliyu Abdulkadir

Gowon ya yabawa marigayi Yar'adua

A wani labarin, kun ji cewa tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon ya yabawa tsohon shugaban kasa, marigayi Umaru Musa Yar'adua.

Gowon ya ce marigayin ya kasance mutum mai gaskiya da rikon amana wanda ba a taba samunsa da cin hanci da rashawa ba.

Wannan na zuwa ne yayin da ake bikin tunawa da marigayin bayan ya cika shekaru 14 da rasuwa a watan Mayun 2010.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel