Bello El-Rufai Ya Bayyana Adadin Miliyoyin da Mahaifinsa Ya Ba Shi da Ya Fito Takara

Bello El-Rufai Ya Bayyana Adadin Miliyoyin da Mahaifinsa Ya Ba Shi da Ya Fito Takara

  • Muhammad Bello El-Rufai ne ya yi wa jam’iyyar APC takarar ‘dan majalisa mai wakiltar Kaduna ta Arewa a zaben 2023
  • Duk da yana sabon ‘dan siyasa, babban yaron gwamnan ya samu karbuwa musamman ganin yadda yake bada taimako
  • A lokacin mahaifinsa ne gwamna a jihar Kaduna, N5m ya ba shi a matsayin gudumuwarsa wajen yakin neman takara a APC

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - Muhammad Bello El-Rufai ya yi wata doguwar hira a watan nan na Maris, inda ya tattauna a game da batutuwa da yawa.

Seun Okinbaloye ya zanta da Hon. Muhammad Bello El-Rufai a shirinsa Mic On, inda ‘dan majalisar ya bada labarin yakin zabensa.

Bello El-Rufai
Hon. Bello El-Rufai da mahaifisa, Nasir El-Rufai Hoto: @B_ElRufai
Source: Twitter

Gudumuwar El-Rufai ga 'dansa a zaben 2023

Kara karanta wannan

Kakakin kwamitin kamfen Atiku ya faɗi muhimman abubuwa 2 da Najeriya ke buƙata kafin zaɓen 2027

‘Dan majalisar mai wakitar Kaduna ta Arewa ya ce a lokacin da yake neman takara a 2023, Naira miliyan biyar mahaifinsa ya ba shi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A lokacin da Bello El-Rufai ya tsaya takarar kujerar majalisar wakilan tarayya, mahaifinsa Nasir El-Rufai shi ne gwamnn Kaduna.

Takarar Bello El-Rufai zuwa majalisar tarayya

A cewar ‘dan majalisar, a lokacin Mai girma Uba Sani yana Sanata, sai ya kawowa gwamnan shawarar takarar Bello El-Rufai a 2023.

Kamar yadda ya shaida a shirin na Podcast, Malam Nasir El-Rufai bai yi maraba da shawarar nan ba saboda wasu dalilai da ya kawo.

El-Rufai ya so takarar yaron da ya haifa?

Daga ciki shi ne tsohon gwamnan na Kaduna bai son ganin ana neman maida mulkin tamkar wani gadon gidan Nasir El-Rufai.

‘Dan majalisar ya kuma ce daga baya mahaifinsa ya bayyana masa yana da saurin fushi, saboda haka bai dace da wakilcin jama'a ba.

An bijiro batun takarar ne a birnin Dubai, Malam Bello El-Rufai ya so a ce gudumuwar yakin zaben da gwamna ya ba da ya wuce N5m.

Kara karanta wannan

Tinubu ya dauko mutumin Buhari ya ba shi shugabancin hukumar kula da almajirai

Bello El-Rufai ya zama wakili a majalisa

Yayin kamfe, Bello El-Rufai ya shiga kowace mazaba da ke Kaduna ta Arewa, kuma a karshe ya tashi da kuri’u fiye da 51, 000 a APC.

Kamar yadda babban yaron gwamnan ya fada, sun yi tsari da kyau, tun kafin ya lashe zabe yake bada tallafi, a karshe ya doke PDP.

‘Dan siyasar ya jero inda suka sha bam-bam da mahaifin nasa, daga ciki shi ne ko kadan Malam El-Rufai bai sha’awar kujerar majalisa.

An hana El-Rufai zama ministan tarayya

A baya ana da labari dan majalisar tarayya, Bello El-Rufai ya fadi yadda ya ji bayan kin amincewa da mahaifinsa ya zama minista.

Nasir El-Rufai ya samu matsala a majalisa yayin tantance wadanda za su zama ministoci, inda aka fake da wani rahoton tsaro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng