Kano: Jami'yyar NNPP Ta Kifar da APC a Zaben Cike Gurbi a Wata Mazaba a Jihar, Bayanai Sun Fito

Kano: Jami'yyar NNPP Ta Kifar da APC a Zaben Cike Gurbi a Wata Mazaba a Jihar, Bayanai Sun Fito

  • Yayin da aka gudanar da zaben cike gurbi a fadin Najeriya, INEC ta fara sanar da sakamakon zaben da aka gudanar
  • Hukumar ta sanar da sakamakon zaben cike gurbi a mazabar Rimin Gado/Tofa a Majalisar jihar Kano
  • INEC ta ayyana Bello Muhammad na jam'iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar Rimin Gado/Tofa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta sanar da sakamakon zaben cike gurbi a jihar Kano.

INEC ta fitar da sanarwar ce kan sakamakon zaben cike gurbi a mazabar Rimin Gado/Tofa a Majalisar jihar Kano.

INEC ta sanar da wanda ya lashe zaben cike gurbi a Kano
Bello Butu-Butu ya lashe zaben cike gurbi a Kano. Hoto: Muhammad Bello.
Source: Facebook

Waye hukumar INEC ta sanar ya lashe zaben?

Kara karanta wannan

Hukumar INEC ta bayyana jami'yyar da ta yi nasara a zaben maye gurbin Gbajabiamila, an fadi kuri'u

Hukumar ta ayyana Bello Muhammad Butu-Butu na jam'iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar Rimin Gado/Tofa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da ya ke sanar da sakamakon zaben, Farfesa Ibrahim Tajo Suraj ya ce jam'iyyar NNPP ta samu kuri'u 31,135 a zaben.

Yayin da jam'iyyar APC mai adawa a jihar da dan takararta suka samu kuri'u 25,577 a zaben da aka gudanar a yau Asabar 3 ga watan Faburairu.

An gudanar da zaben cike gurbi a jihohi 26

A yau ne aka gudanar da zaben cike gurbi a fadin kasar baki daya wanda ya kunshi jihohi 26 da ke Najeriya.

Har ila yau, Hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta sanar da wanda ya yi nasara a zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar Legas.

Hukumar ta bayyana Fuad Laguda na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar Surulere a Majalisar Wakilai.

INEC ta sanar da Ehindero wanda ya lashe zabe

Kara karanta wannan

Kano: An gano wadanda suka dauki nauyin ta'addanci a zaben cike gurbin jihar, NNPP ta yi martani

Kun ji cewa Hukumar zabe ta INEC ta sanar da wanda ya lashe zabe a mazabar Akoko da ke jihar Ondo a Majalisar Tarayya.

Hukumar ta ayyana Ifeoluwa Ehindero na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar.

Faresa Johnson Fasinmirin shi ya ayyana Ehindero a matsayin wanda ya lashe zaben bayan kammala tattara sakamakon zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.