Kano: Ko Yanzu Sun Shiga Taitayinsu, Kwankwaso Ya Bugi Kirji da Yawan Jama’a a Zabe
- Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya bayyana yadda suka nuna wa duniya yawan jama’a
- Kwankwaso ya ce ko ba komai su ba kowa ba ne amma sun tabbatarwa duniya cewa suna da jama’a
- Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabri ya samu nasara a Kotun Koli a ranar Juma’a da ta gabata
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano – Sanata Rabiu Kwankwaso a sake martani bayan nasarar Gwamna Abba Kabir a Kotun Koli.
Kwankwaso ya ce ko yanzu sun nuna wa duniya cewa suna da jama’a wanda hakan ya yi tasiri a nasararsu.

Source: Twitter
Mene Kwankwaso ke cewa a Kano?
Sanata Kwankwaso ya bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo da ya karade shafukan sadarwa.

Kara karanta wannan
Bayan sha da kyar a kotu, Gwamnan PDP ya bugi kirji bayan nasara a shari'o'i 38 kan zabe, akwai dalili
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce su a ‘yan siyasa ba alkalai ba ne kuma ba sojoji ko ‘yan sanda ba amma sun nuna wa duniya jama’a nasu ne.
Ya kara da cewa ko a 2003 akwai damar da za su kwace amma suka bari duk da sun sani an musu rashin adalci.
Hakurin da suka yi shekarar 2003?
Ya ce:
“Mu a ‘yan siyasa alkalai ne? mu sojoji ne? mu ‘yan sanda ko INEC ne?, amma dai mun nuna wa duniya cewar jama’ar dai namu ne.
“Ko a 2003 da aka zo rigingimu, muna da damar da za a yi irin wadannan abubuwa na kwata, tabbas ba a yi amana adalci ba amma mun yi hakuri.”
Sanatan ya ce haka su ka yi hakuri abin ya wuce da haka saboda a zauna lafiya har wasu suke cewa gwara ma da Allah ya saka suka fadi saboda damar da suka samu daga baya.

Kara karanta wannan
Kano: Kwankwaso Ya faɗi makircin da aka Shirya ƙulla masa idan Gawuna ya yi nasara a Kotun Koli
Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir ya yi nasara a Kotun Koli a ranar Juma’a 12 ga watan Janairu.
Kwankwaso ya magantu kan masarautun Kano
A wani labarin, Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi magana kan halin da ake ciki game da masarautun Kano.
Kwankwaso ya ce tabbas dole za a zo ayi zama kan wadannan masarautun ganin yadda aka kirkire su.
Wannan na zuwa ne bayan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje ya kirkiro masarautun a jihar.
Asali: Legit.ng