Kano: Ko Yanzu Sun Shiga Taitayinsu, Kwankwaso Ya Bugi Kirji da Yawan Jama’a a Zabe

Kano: Ko Yanzu Sun Shiga Taitayinsu, Kwankwaso Ya Bugi Kirji da Yawan Jama’a a Zabe

  • Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya bayyana yadda suka nuna wa duniya yawan jama’a
  • Kwankwaso ya ce ko ba komai su ba kowa ba ne amma sun tabbatarwa duniya cewa suna da jama’a
  • Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabri ya samu nasara a Kotun Koli a ranar Juma’a da ta gabata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano – Sanata Rabiu Kwankwaso a sake martani bayan nasarar Gwamna Abba Kabir a Kotun Koli.

Kwankwaso ya ce ko yanzu sun nuna wa duniya cewa suna da jama’a wanda hakan ya yi tasiri a nasararsu.

Kwankwaso ya bugi kirji kan yawan jama'a da suke da shi a Kano
Kwankwaso ya yi alfahari da yawan jama'a da suke da shi a Kano. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso.
Asali: Twitter

Mene Kwankwaso ke cewa a Kano?

Sanata Kwankwaso ya bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo da ya karade shafukan sadarwa.

Kara karanta wannan

Bayan sha da kyar a kotu, Gwamnan PDP ya bugi kirji bayan nasara a shari'o'i 38 kan zabe, akwai dalili

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce su a ‘yan siyasa ba alkalai ba ne kuma ba sojoji ko ‘yan sanda ba amma sun nuna wa duniya jama’a nasu ne.

Ya kara da cewa ko a 2003 akwai damar da za su kwace amma suka bari duk da sun sani an musu rashin adalci.

Hakurin da suka yi shekarar 2003?

Ya ce:

“Mu a ‘yan siyasa alkalai ne? mu sojoji ne? mu ‘yan sanda ko INEC ne?, amma dai mun nuna wa duniya cewar jama’ar dai namu ne.
“Ko a 2003 da aka zo rigingimu, muna da damar da za a yi irin wadannan abubuwa na kwata, tabbas ba a yi amana adalci ba amma mun yi hakuri.”

Sanatan ya ce haka su ka yi hakuri abin ya wuce da haka saboda a zauna lafiya har wasu suke cewa gwara ma da Allah ya saka suka fadi saboda damar da suka samu daga baya.

Kara karanta wannan

Kano: Kwankwaso Ya faɗi makircin da aka Shirya ƙulla masa idan Gawuna ya yi nasara a Kotun Koli

Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir ya yi nasara a Kotun Koli a ranar Juma’a 12 ga watan Janairu.

Kwankwaso ya magantu kan masarautun Kano

A wani labarin, Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi magana kan halin da ake ciki game da masarautun Kano.

Kwankwaso ya ce tabbas dole za a zo ayi zama kan wadannan masarautun ganin yadda aka kirkire su.

Wannan na zuwa ne bayan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje ya kirkiro masarautun a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.