Kotun Koli Ta Yi Hukuncin Karshe a Shari'ar Neman Tumbuke Gwamnan Gombe, Ta Fadi Dalillai

Kotun Koli Ta Yi Hukuncin Karshe a Shari'ar Neman Tumbuke Gwamnan Gombe, Ta Fadi Dalillai

  • Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan takaddamar zaben gwamnan jihar Gombe a Najeriya
  • Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya na jam'iyyar APC a matsayin halastaccen gwamna
  • Kotun kuma har ila yau, ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Jibrin Barde saboda rashin hujjoji

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jam'iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar.

Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan Gombe
Kotun Koli ta tabbatar da nasarar Inuwa Yahaya. Hoto: Jibrin Barde, Inuwa Yahaya.
Source: Facebook

Wane hukunci kotun ta yanke a zaben Gombe?

Har ila yau, kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Muhammad Jibrin Barde saboda rashin gamsassun hujjoji.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta sake yanke hukuncin karshe kan shari'ar neman kifar da gwamnan Kebbi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin hukuncin, jagoran alkalan guda biyar, Mai Shari'a, Kudirat Kekere-Ekun ta yi watsi da korafe-korafen Jibrin Barde kamar yadda Kotun Daukaka Kara ta yi.

Ta ce korafe-korafen da dan takarar PDP ya gabatar a gaban kotun ba su da tushe bare makama da za a yi amfani da su, cewar TheCable.

A baya, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya na APC a matsayin zababben gwamnan jihar.

Martanin kotun kan korafe-korafen PDP

Yayin da kuma ta yi watsi da karar Jibrin Barde wanda ya yi takara a jam'iyyar PDP a zaben na watan Maris, cewar The Nation.

Tun farko, Hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya a matsayin wanda ya lashe zaben.

Dan Barde a bangarensa, ya kalubalanci zaben da aka gudanar a watan Maris da cewa akwai kura-kurai cike a ciki.

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da sauraran shari'ar zabukan jihohi da dama a Kotun Koli da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan shari'ar neman tsige gwamnan APC, akwai dalilai

Kotun Koli ta yi hukunci a zaben jihar Kebbi

Kun ji cewa Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Kebbi a yau Juma'a.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris na jami'yyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.

Yayin da ta yi watsi da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP a zaben, Aminu Bande saboda rashin gamsassun hujjoji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.